Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 08/10/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 08/10/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Habiba Adamu da Aisha Babangida

  1. An samu raguwar kwararar baƙin haure cikin Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu alƙaluma na Amurka sun nuna cewa an samu gagarumar raguwar kwararar bakin haure tsakanin iyakar ƙasar da Mexico mafi girma a tsawon shekara 50.

    Alƙaluman da kafar yaɗa labarai ta CBS ta samu, sun nuna cewa tsakanin 2024 zuwa shekarar 2025, jami'an Amurka sun hana baƙin haure sama da 238,000 tsallakawa kan iyakar ƙasar.

    Lokacin ya ƙunshi watanni huɗu na mulkin shugaba Joe Biden.

    Bayanan sun nuna cewa watanni takwas na farkon mulkin Trump, an samu baƙin haure da suka tsallako ƙasa da 9000 a duk wata.

    Fadar White House ta ce alƙaluman sun tabbatar da alƙawarin shugaba Trump na tabbatar da tsaron iyakar Amurka.

  2. Za a karɓe wa ƴan Najeriyar da aka samu da laifi a waje fasfo na shekara 10

    ,,,,

    Asalin hoton, Nigerian Immigration Service

    Majalisar dattawan Najeriya ta amince a haramta wa duk wani ɗan ƙasar da aka samu da aikata laifi a ƙasashen waje, yin amfani da fasfon Najeriya na tsawon shekara 10.

    Majalisar ta amince da hakan ne a yayin zaman da ta yi a Abuja, a ranar Talata

    Sanata Abubakar Bello mai wakiltar jihar Neja ta arewa ne ya gabatar da ƙudurin a gaban majalisar, a wani ɓangare na yi wa dokar fasfo ɗin garambawul.

    Ƙudurin ya buƙaci a karɓe fasfo ɗin ne na tsawon shekara 10 mafi ƙaranci, abun da suke ganin zai taimaka wajen sanya ƴanƙasar da ke waje kuma suke aikata manyan laifuka shiga taitayinsu.

    Ƴan majalisar na fatan matakin zai taimaka wajen magance ɓata sunan ƙasar da wasu ke yi a ƙasashen ƙetare.

  3. Surukin Trump da wakilin Amurka na musamman za su shiga tattaunawar Hamas da Isra'ila

    ,,,

    Wakilin na musamman na Amurka, Steve Witkoff da kuma surukin shugaban Amurka, Jared Kushner za su shiga cikin tattaunawar zaman lafiya da ake yi tsakanin Isra'ila da Gaza a Masar, a ranar Laraba.

    Sun isa Masar ɗin ne bayan rana ta biyu ta tattaunawar ba ta haifar da wani sakamakon da ya taka kara ya karya ba, kamar yadda wani ƙusa a jami'an Falasɗinawa wanda ke da masaniya kan tattaunawar ya shaida wa BBC.

    Hakan na zuwa ne yayin da masu shiga tsakani daga wasu manyan ƙasashen duniya za su shiga tattaunawar tsakanin Isra'ila da Hamas don kawo ƙarshen yakin Gaza, yayin da aka shiga kwana na uku ana tattaunawa.

    Tuni wakilin Firaministan Isra'ila da ministan harkokin wajen Qatar da shugaban hukumar leƙen asirin Turkiya suka isa don shiga tattaunawar.

    Wakiliyar BBC ta ce da yake jawabi a wata kafar talbijin ta Masar, shugaban Hamas ya ce a shirye suke a cimma yarjejeniya amma kuma suna buƙatar tabbaci.

    Shugaba Trump kuma ya sha alwashin tabbatar da yarjejeniyar idan har aka amince da tsagaita wuta.

    Sai dai Firaiminista, Benjamin Netanyahu bai yi tsokaci kan tattaunawar ba, amma ya shaida wa ƴan ƙasarsa cewa ana cikin " ranakun fatan yanke hukunci."

  4. Muna son a kafa kwamitin da zai zaɓi sabon shugaban INEC - Jam'iyyun siyasa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jam'iyyun siyasa a Najeriya sun fara martani kan saukar shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Inec Farfesa Mahmood Yakubu daga mukaminsa bayan kawo karshen wa'adinsa na biyu

    Kwamitin tuntuɓa tsakanin jam'iyyun Najeriya ya yi kiran samar da wani kwamitin da zai jagoranci nada sabon shugaban hukumar zaɓe ta Inec da kuma kwamishinoni.

    A ranar Talata ne Farfesa Mahmood Yakubu ya sauka daga muƙaminsa na shugaban hukumar zaɓen Najeriya tare da miƙa ragamar jagorancin Inec ga May Agbamuche kafin naɗa sabon shugaba.

    Shugaban ƙasa ne kundin tsarin mulki ya ba damar zaɓen shugaban hukumar zaɓe bayan tuntubar majalisar ƙasa da ta ƙunshi tsoffin shugabanni da gwamnoni da shugabanannin majalisun tarayya.

  5. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a yau Laraba.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kuma kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.