Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 28 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed, Aisha Babangida da Ahmad Bawage

  1. An kai wa ƴarmajalisar Amurka Ilhan Omar hari a Minneapolis

    Ilhan

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Wani mutum ya kai wa fitacciyar 'yar majalisar wakilan nan ta jam'iyyar Democrat a Amurka, Ilhan Omar, hari a lokacin da take gabatar da jawabi a wani taron wayar da kan jama'a a birnin Minneapolis.

    'Yansanda sun ce mutumin ya yi amfani da sirinji ne wajen fesa mata wani ruwa da ba a san ko mene ne ba.

    Ilhan wadda ta ci gaba da gudanar da jawabinta, ta ce ba za ta zuba ido tana kallon wadanda ta bayyana a matsayin karnukan farautar Trump su hana ta magana ba.

    Wakiliyar BBC Ana Faguy, na cikin dakin taron lokacin da abun ya faru. Ta ce ''na ji shi mutumin na ta cewa tana so ne ta hada mu fada da juna, yayin da ake kokarin fitar da shi daga dakin taron.''

    Wurin ya dan yi shiru, kafin daga bisani aka ci gaba da gudanar da taron.

  2. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.