Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 22/02/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, Lahadi, 22/02/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Annur Muhammad da Isiyaku Muhammed

  1. Mali na binciken zargin sojojinta da kashe fararen hula 24

    Mali

    Asalin hoton, AFP

    Rundunar sojin ƙasa na Mali ta ƙaddamar da bincike kan zargin da ake yi wa jami'anta na kashe fararen hula aƙalla 24 a arewan ƙasar a ranar Litinin.

    Zargin ya fito ne daga ƙungiyar ƴantawayen Azawad Liberation Front da ke rigima da gwamnatin ƙasar, inda ta zargi sojojin ƙasar tare da haɗin gwiwar sojojin haya na Wagner da kama motoci biyu na fasinja a ranar 17 ga Fabrairu, sannan suka kashe fararen hula da ke cikin motar, ciki har da mata da ƙananan yara waɗande suke hanyarsu ta zuwa Algeria daga birnin Gao na ƙasar.

    A wata sanarwa da babban hafsan sojin ƙasar Mali, Janar Oumar Diarra ya fitar, ya ce zargin, "wanda ƴanta'adda da masu goyon bayansu suka fitar, yunƙurin ɓata wa ƙasar suna ne."

    "Rundunar sojin ƙasar za ta buɗe bincike kamar yadda take gudanar da wani binciken kan zargin sojojinta da kashe wasu mutum bakwai fararen hula a wata mota ƙirar Hilux a yankin Doma a ranar 2 ga Janairun 2025," in ji shi.

    An dai daɗe ana gwabzawa tsakanin gwamnatin Mali da ƴan tawayen Tuareg da ke arewacin ƙasar.

  2. KACRAN ta yaba wa Sarkin Musulmi bisa ƙoƙarin samar da zaman lafiya da haɗin kai

    Khalil Moh’d Bello

    Asalin hoton, Khalil Moh’d Bello

    Ƙungiyar makiyaya ta Kulen Allah Cattle Rearers Association of Nigeria (KACRAN) ta yaba wa Mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar bisa jajircewarsa wajen samar da zaman lafiya da haɗin kai a faɗin Najeriya.

    KACRAN ta ce a daidai lokacin da watan Ramadan ke ƙaratowa, hakan nk nufin sarkin na cika shekara 10 a karagar mulki.

    Wannan jawabin na ƙunshe a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, wadda ke ɗauke da sa hannun shugabanta na ƙasa, Khalil Moh’d Bello.

    KACRAN ta bayyana wasu abubuwa da ta ce suna cikin nasarorin da sarkin na musulmi ya samu a shekara 10 da ya yi yana sarauta, inda ta ce, "ya taimaka wajen haɗa kan musulmi da ƙarfafa ƙungiyar JNI da samar da haɗin kai tsakanin addinai mabambanta.

    "KACRAN ta yaba da ƙoƙarin Sultan wajen bayar da shawarwari domin tabbatar da zaman lafiya da tabbatar da adalci ga dukkan ƴan Najeriya ba tare da la'akari da bambancin addini ko ƙabila da ɓangaranci ba," kamar yadda suka bayyana a wata sanarwa, sannan suka yaba masa bisa rashin shiga harkokin siyasa ya ƙara masa daraja.

  3. Kasuwar crypto ta yi ƙasa warwas

    ByBit

    Asalin hoton, Getty Images

    Kasuwar crypto ta yi mummunar faɗi bayan masu kutse sun yi satar da ake ganin ita ce mafi girma a tarihin harkar hada-hadar kuɗin na intanet.

    A ranar Juma'a ce kamfanin hada-hadar crypto na Dubai, ByBit ya sanar da cewa an masa kutse, inda aka sace masa crypto da ƙimarsa ya kai dala biliyan 1.5.

    Kamfanin ya ce masu kutsen sun kutsa ne cikin hada-hadar kuɗin crypto na Ethereum, sannan suka wawushe shi suka tura wani wajen daban.

    Sai dai kamfanin ya buƙaci abokan hulɗarsa da su kwantar da hankalinsu, inda ya ce zai mayar da asara.

    Tun bayan da Donald Trump ya ɗare kan karagar mulki ne kasuwar crypto take kwan-gaba-kwan-baya.

  4. PDP ta lashe zaɓen dukkan ƙananan hukumomin jihar Osun 30

    Osun

    Asalin hoton, Other

    Jam'iyyar PDP ta lashe zaɓukan dukkan ƙananan hukumomi guda 30 da na kansilolinsu na jihar Osun da ke kudu maso yammacin Najeriya.

    Tashar Channels ce ta ruwaito hakan, inda ta ce shugaban hukumar zaɓen jihar mai zaman kanta, Hashim Abioye ne ya sanar da sakamakon a wani taron ganawa da manema labarai da ya yi a jihar.

    Tun farko dai an ta samun takon saƙa-tsakanin gwamnatin jihar da ƴansanda da ma ministan shari'a na Najeriya.

    Ministan ya buƙaci a dakatar da zaɓen, sannan ƴansanda suka ce sun samu bayanan sirri kan yiwuwar tayar da hargitsi, don haka suka yi kira ga gwamnan da ya dakatar da yunƙurinsa na gudanar da zaɓen, lamarin shi kuma ya ce babu gudu, babu ja da baya kan zaɓen.

  5. 'Ƴanbindiga sun kwashe mana shanunmu baki ɗaya a garin Gurgurawa na Zamfara'

    Shanu

    Asalin hoton, Harry Hook

    A Najeriya, wasu Fulani makiyaya da suka kwashe fiye da shekara ɗari, suna zaune a rugagen Gurgurawa na yankin ƙaramar hukumar Gusau a jihar Zamfara, sun auka cikin tsaka mai wuya, sakamakon yawan hare-haren da ƴanbindiga suke kai masu, har sai da maharan suka raba su da illahirin shanunsu.

    Makiyayan, waɗanda suke zaman makoki a rugagensu da ke Gurgurawa, sun kuma bayyana cewa an yi wa wasu mutanensu kisan gilla, wanda Alhaji Muhammadu Makau, Sarkin Fulanin yankin Gusau ya ce da rana tsaka aka kashe su.

    Sarkin Fulanin ya ce wannan abu da ya zo masu da ba-zata, ya ƙara jefa su cikin halin tsaka mai wuya.:

    BBC ta tuntuɓi Mustafa Jafaru Ƙaura, babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar ta Zamfara, kan kafafen watsa labarai da al'amuran jama'a, inda ya ce a kira jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan jihar ta Zamfara, Yazid Abubakar, kuma an kira layin wayarsa, amma bai amsa ba.

    Sai dai wasu majiyoyin tsaro a jihar, sun tabbatar wa BBC aukuwar lamarin. Amma ɗaya daga cikinsu ta musanta sa hannun jami'an tsaro a cikin lamarin, amma ta ce ana nan ana gudanar da bincike.

  6. APC ta ayyana ranar gudanar da taron masu ruwa da tsaki

    Ganduje

    Asalin hoton, Aminu Dahiru Ahmad/Facebook

    Jam'iyyar APC ta saka ranar Talata 25 ga watan Fabrairu da Laraba, 26 ga Fabrairu domin gudanar da taron masu ruwa da tsaki, da kuma babban taronta.

    Sakataren jam'iyyar na ƙasa, Surajuddeen Bashiru ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a a Abuja.

    Sanarwar ta ce za a yi taron masu ruwa da tsakin a daƙin taro na Banquet da fadar shugaban ƙasar Najeriya, sannan a gudanar da babban taron jam'iyyar a ranar Laraba a sakatariyar jam'iyyar da ke Abuja.

  7. Atiku ya yaba wa gwamnan Osun bisa gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi duk da gargaɗin ƴansanda

    Atiku

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a jam'iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya yaba wa Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke bisa gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar, duk da gwamnatin tarayya da ƴansanda sun buƙaci a dakatar da zaɓen.

    Tun da farko dai ministan shari'a na Najeriya, Lateef Fagbemi ne ya yi kira ga gwamnan jihar da ya dakata da zaɓen, domin a cewarsa, wa'adin tsofaffin ƙananan hukumomin bai ƙare ba.

    Sannan kuma ƴansanda sun yi gargaɗin cewa a dakata da gudanar da zaɓen saboda hukuncin wata kotu, da kuma bayanin sirri da suka samu kan yiwuwar tayar da hargitsi.

    Sai dai alamu sun nuna gwamnan ya yi watsi da gargaɗin, inda mutanen jihar suka fito domin kaɗa ƙuri'a a zaɓen.

    Domin haka ne Atiku ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce, "a daidai lokacin da mutanen jihar Osun suka fito domin kaɗa ƙuri'ar zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi, ina sake kira gare su da gudanar da zaɓen cikin lumana. Shugabannin ƙananan hukumomin su ne ƙashin bayan dimokuraɗiyya saboda kusancinsu ga al'umma.

    "Ina yaba wa gwamnan Osun Ademola Adeleke bisa gudanar da zaɓen, sannan ina kira ga jami'an tsaro da masu sanya ido a akwatunan zaɓe su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa."

  8. Jagoran ƴan adawan Uganda ya kawo ƙarshen yajin cin abinci

    Uganda

    Asalin hoton, AFP

    Jagoran ƴan adawa a Uganda Kizza Besigye ya kawo ƙarshen yajin cin abincin da yake yi.

    Lauyansa ya ce ya yanke shawarar daina yajin cin abincin saboda a hukumance an gurfanar da shi gaban wata kotun farar hula.

    Ana zargin Mr Besigye da cin amanar ƙasa, wanda ya musanta hakan, wanda idan aka same shi da laifi zai iya fuskanta hukuncin kisa.

    Ana tsare da Mr Besigye, wanda tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a ƙasar ta Uganda, tun bayan ɓatan dabon da ya yi a ƙasar Kenya.

  9. Gobe Lahadi za a gudanar da zaɓe a Jamus

    Jamus

    Asalin hoton, Getty Images

    An shiga rana ta ƙarshe ta gangamin yaƙin neman zaɓen gama gari a ƙasar Jamus.

    A gobe Lahadi ne Jamusawa za su fita runfunan zaɓe, Jam'iyyar The conservative Christian Democrats da Friedrich Merz ke jagoranta na sahun tun kafin ranar zaɓen, yayin da ake hasasshen jam'iyyar AFD ka iya zama ta biyu, sai SPD ta Olaf Scholz.

    Wakilin BBC ya ce masu kaɗa ƙuri'a sun ce suna son kwanciyar hankali da shugabanci na gari, musamman kan halin da Jamus ke ciki.

    Gangamin yaƙin neman zaɓen dai ya maida hankali kan batun bunƙasa tattalin arziki, sai batun ƴan-cirani ya kunno kai bayan ƙaruwar hare-haren da masu neman mafaka ke kai wa.

    A baya-bayan nan kuma ƴan takarar sun maida hankali kan kan tsaro da manufofin shugaba Trump na Amurka na lallaɓa Rasha na kawo ƙarshen yaƙi tsakaninta da Ukraine.

  10. 'Yan Israila da Hamas ta saki sun fito daga tsananin azaba - Shugaban Isra'ila

    Isaac Herzog

    Asalin hoton, OTHERS

    Shugaban ƙasar Isra'ila ya ce ya ji daɗi sosai ganin yadda aka saki 'yan ƙasarsa da Hamas ta yi garkuwa da su, da safiyar nan ta Asabar.

    A wani sako da rubuta a shafinsa na X, Isaac Herzog, ya ce, ''sun komo daga tsananin azaba za su fara zaman jinya da farfaɗowa tare da iyalansu ababen ƙaunarsu, waɗanda suka yi gwagwarmaya iya ƙarfinsu a kansu.

    Mista Herzog ya ƙara da cewa komawar duka waɗanda aka yi garkuwa da su ba da ɓata wani lokaci ba , abu ne mai muhimmanci.

    Ya ce, ''dole mu yi duk abin da zai yuwu mu dawo da dukkanin mutanen da aka yi garkuwa da su a Gaza - har zuwa na ƙarshensu.''

    Haka kuma ya nuna jimami da jajantawa a kan Shiri Bibas, 'yar Isra'ila da Hamas ta bayar da wata gawa, wadda iyalanta suka ce ba tata ba ce ranar Alhamis, inda daga baya a jiya Juma'a suka miƙa ainahin gawar tata.

  11. Falasɗinawa 602 Isra'ila za ta saki a musayar Yahudawa shida yau

    Wani Bafalasɗine da Isra'ila ta saki tare da iyalansa

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumomin Isra'ila za su saki Falasɗinawa ɗari shida da biyu ne a musayar 'yan ƙasarta shida da Hamas za ta saki a yau Asabar.

    Tuni Hamas ta riga ta saki biyar daga cikin 'yan Isra'ila shida da za ta saki a yau ɗin cikin waɗanda ta yi garkuwa da su.

    Ɗan Isra'ila cikon na shida da Hamas ɗin za ta saki nan gaba a yau shi ne Hisham al-Sayed, wanda za a saki ba tare da wani taron jama'a ba, kamar yadda bayanai suka nuna.

    Hamas ta kama shi ne tun shekara ta 2015 bayan da ya shiga yankin Gaza.

    Rahotanni na nuna cewa tuni Red Cross ta danƙa wa rundunar sojin Isra'ila wasu daga cikin Yahudawan da aka saki yau, kuma sun shiga yankin Isra'ila.

    Falasɗinawan da Isra'ila za ta saki 602 a yau, na daga matakin farko na yarjejeniyar dakatar da wuta, wadda ta tanadi cewa Isra'ila za ta saki Falasɗinawa fursunoni da waɗanda take tsare da su 1,900 a musaya da 'yan Isra'ila 33 da Hamas ta yi garkuwa da su.

    An saki sama da Falasɗinawa fursunoni 1,000 da Isra'ila take tsare da su, tun bayan da aka fara aiwatar da kashin farko na yarjejeniyar mai mataki uku, daga ranar 19 ga watan Janairun 2025.

    Hukumomin Falasɗinu sun ce a makon da ya gabata Isra'ila ta saki fursunoni Falasɗinawa 369 - kuma 36 daga cikinsu na zaman ɗaurin rai da rai ne sannan ana tsare da 333 ba tare da wata tuhuma ba.

    Yawancin Falasɗinawan da ta saki an kai su Gaza wasu an sake su ne a Gaɓar Yamma sannan galibin masu hukuncin ɗaurin rai da rai an fitar da su ne zuwa Masar.

    Tun bayan harin ba-zata da Hamas ta kai wa Isra'ila a 2023, yawan Falasɗinawan da Isra'ila ke tsare da su ya ninka biyu zuwa wajen 10,000

  12. Hamas ta saki ƙarin Isra'ilawa uku a Gaza

    Mayaƙan Hamas da 'yan Isra'ila uku da za a saki

    Asalin hoton, Reuters

    Bayan sanya hannu a dakardu tsakanin Hamas da wakiliyar ƙungiyar Red Cross, Hamas ta saki ƙarin mutum uku cikin waɗanda aka tsara za ta saki yau Asabar, 'yan Isra'ila da ta yi garkuwa da su.

    A wannan rukunin na mutum uku mayaƙan ƙungiyar sun fara sakin mutum na farko Eliya Cohen mai shekara 27.

    Sai kuma suka saki Omer Shem Tov mai shekara 22 da kuma na uku Omer Wenkert, mai shekara 23, waɗanda Hamas ta kama su a bikin waƙe-waƙe na Nova, ranar 7 ga watan Oktoba na 2023, inda aka danƙa su ga ƙungiyar Red Cross a yau ɗin.

    A wannan karon ana miƙa su ne a garin Nuseirat, wanda ke tsakiyar Zirin Gaza.

    Bayahude na huɗu da aka tsara Hamas ɗin za ta saki yau shi ne Hisham al-Sayed, wanda ta yi garkuwa da shi tun 2015 bayan da ya tsallaka zuwa Gaza shi kaɗai.

    Za kuma a sake shi ne nan gaba a yau ba tare da wani gangamin jama'a ba.

    Ana sa ran Isra'ila za ta saki Falasɗainawa sama da 600 daga cikin waɗanda take tsare da su a gidajen yarinta a madadin Yahudawa huɗu da Hamas ke saki yau.

  13. Falasɗinawa sun taru a Nuseirat a Gaza don kallo

    Taron Falasdinawa

    Asalin hoton, Reuters

    Falasɗinawa sun taru a Nuseirat, inda nan ne za a saki 'yan Isra'ilan rukuni na biyu nan gaba yau a Zirin na Gaza.

    Nuseirat na nisan kilomita biyar ne a arewa maso gabashin Deir al-Balah, wanda birni ne a tsakiyar Zirin Gaza.

  14. Yadda Red Cross ta taimaka wajen fitar da Isra'ilawa biyun da aka saki daga Gaza

    Taron mutane da mayaƙan Hamas da motocin Red Cross

    Asalin hoton, Reuters

    Tattaunawar ta fara ne da waya da kuma waje.

    Da zaran Red Cross ta samu cikakken bayani a wannan waya, sai ta tura jami'anta a motoci masu ɗauke da tambarin ƙungiyar domin ɗauko Isra'ilawan a Gaza.

    Su ma sojojin Isra'ila da jami'an lafiya an girke su a wurare da dama domin karɓar mutanen su mayar da su gida.

    Mai magana da yawun ƙngiyar ta Red Cross Sarah Davies ta gaya wa BBC cewa, '' za a ga aikin kamar mai sauƙi amma a gaskiya yana da sarƙaƙiya da buƙatar tsauraran matakan tsaro domin taƙaita haɗari ga waɗanda ke cikin aikin.

    Ƙungiyar wadda ke shiga tsakani wajen musayar mutanen tsakanin Isra'ila da Hamas ta sanya ayarin ƙwararru, wasu daga cikin an taɓa irin wannan aikin da su a baya - kodayake an ce wannan ya fi tsanani a kan na baya.

    Akwai wasu bayanai da ƙungiyar ba za ta faɗa ba a fili saboda hakan ka iya yin tazgaro ga matakan tsaron da aka tsara.

    Davies ta ce sun tsara hanyoyi daban-daban da za su riƙa bi zuwa sassan na Gaza, saboda sun san a ko wane lokaci za a iya sauya hanya kan wadda ta fi rashin haɗari.

    Daga cikin babban abin da ke damun ƙungiyar ta Red Cross a wannan aiki shi ne -haɗarin bama-baman da ba su fashe ba da wuraren da aka lalata da kuma tarin mutane da ke cike da damuwa.

  15. Isra'ilawa na murna a Tel Aviv yayin da Hamas ta saki 'yan ƙasar biyu

    Taron mutane

    Asalin hoton, Reuters

    Jama'a sun taru a Dandalin Tsararru (Hostages Square), da ke babban birnin ƙaar Isra'ila, Tel Aviv, suna kallon yadda aka saki mutum biyu da Hamas ta saki ta danƙa wa Red Cross.

    Mutane da yawa na riƙe da hotunan waɗanda aka saki.

  16. Sojin Isra'ila sun ce mutum biyu da Hamas ta saki yau sun isa ƙasar

    Daya daga cikin wadanda hamas ta saki

    Asalin hoton, Reuters

    Rundunar sojin Isra'ila ta tabbatar da cewa 'yan ƙasar biyu da Hamas ta saki a yau Asabar ,a yanzu sun shiga yankin ƙasar

    A wata sanarwa sojin da kuma hukumomin leƙen asiri na Isra'ilar sun ce mutanen na kan hanyarsu ta sa cibiyar musamman da aka tanada a kudancin Isra'ila, inda za a haɗa su da iyalansu.

    Sanarwar ta ƙara da cewa rundunar sojin Isra'ila, IDF, na shirin karɓar ƙarin mutum huɗu da Hamas za ta saki a yau ta hannun ƙungiyar agaji ta Red Cross.

  17. Red Cross ta danƙa wa sojin Isra'ila mutum biyu da Hamas ta saki

    Lokacin da Hamas take sakin 'yan Isra'ila biyu

    Bayanan da muke samu a yanzu haka na nuna cewa Hamas ta saki Isra'ilawa biyu daga cikin shida da za ta saki a yau Asabar.

    Mutanen biyu da aka saki a Rafah, kudancin Gaza, Avera Mengistu da Tal Shaham, a yanzu ƙungiyar agaji ta Red Cross da ke shiga tsakani a musayar ta danƙa su a hannun rundunar sojin Isra'ila.

    Hamas ta kama Avera Mengistu a 2014 bayan da ya tsallaka Gaza shi kuwa Tal Shoham mai shekara 40, ya shiga hannun Hamas ne a ranar 7 ga watan Oktoba 2023, daga Kibbutz Be'eri.

    Nan gaba a yau ɗin ne ake sa ran Hamas za ta saki ragowar huɗu, yayin da ita ma Isra'ila za ta sako ɗaruruwan fursunoni Falasɗinawa da take tsare da su, kamar yadda yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta a Gaza ta tanada.

  18. Yau Hamas za ta sake sakin Isra'ilawa da take garkuwa da su

    'Yan Isra'ila

    Asalin hoton, Reuters

    Nan gaba a yau Asabar ake sa ran Hamas za ta saki ƙarin Isra'ilawa shida daga cikin mutanen da ta yi garkuwa da su, a ci gaba da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.

    Rahotanni na cewa iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su na jiran ganin 'yan uwan nasu a raye.

    Hudu daga ciki Hamas ta cafke su ranar 7 ga watan Oktobar 2023, yayin da sauran biyun ta jima da kama su a Gaza.

    Wannan karon ana sa ran Isra'ila za ta sako sama da Falasɗinawa 600 da take tsare da su domin musayarsu da Isra'ilawan 6.

    Hamas ta sake miƙa gawar da ta ce ta Shiri Bibas ce, amma Isra'ila na binciken kwayar halitta don tabbatar da hakan.

  19. Buɗewa

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafin da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, muna muku maraba a wannan safiya ta Asabar 22 ga watan Fabarairun 2025.

    Za mu kasance da ku daga yanzu zuwa wani lokaci a nan gaba.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu da sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo, har ma ku yi muhawara.

    Mu fara da wannan karin maganar - Ɗanyen kasko ba ya kai ruwan wanka banɗaki