Ƴan sanda sun bayyana cewa, an kashe aƘalla mutum 18 a jihar Neja, dake yankin Arewa ta tsakiyar Najeriya, sakamakon jerin hare-haren da ke da nasaba da dogon rikici tsakanin manoma da makiyaya.
Kakakin rundunar ƴan sandan jihar, Wasiu Abiodun, ya ce jami’ai sun samu rahoto daga yankin Katako na ƙaramar hukumar Rafi cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari ƙauyen Godoro a daren ranar Litinin.
Ya ce an harbe wani matashi mai shekara 25 har lahira, lamarin da ya sa mambobin ƙungiyar sa-kai ta yankin suka tare hanya tare da kashe wani mutum mai shekaru 28 a matsayin ramuwar gayya.
Ƴan sanda sun ce a wani lamari na daban a ranar Talata da daddare, an kona mutane 15 har lahira a wani gida mai ɗakuna biyu a Angwan-Baago kusa da ƙauyen Godoro, yayin da aka kashe wani mutum a wani wuri na daban, wanda ya kawo adadin mace-macen da aka tabbatar ya kai aƙalla 18.
Duk da haka, majiyoyin yankin sun ce jimillar waɗanda suka mutu na iya kai wa 48 bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya.
Wani mazaunin yankin, Hamza Maisaje Kwana, ya ce "Ko da yake ba za mu iya tabbatar da ainihin adadin waɗanda abin ya shafa ba, kiyasinmu ya nuna cewa an kashe mutane 43," in ji shi.
Ƴansakai ƙungiya ce wadda galibi ta kunshi Hausawa manoma a arewacin Najeriya.
An kafa su ne a yankin don kare al'ummomi daga Ƴan fashin daji.
Duk da haka, an kuma zarge su da aikata kisan kai da cin zarafi ga makiyaya Fulani ba bisa ƙa'ida ba.
A na su ɓangaren kuma wasu Fulani makiyaya sun kafa nasu ƙungiyoyin.
Tashe-tashen hankula makamantan wannan sun ja hankalin ƙasashen duniya a cikin ƴan shekarun nan, inda al'ummomi daban-daban ke zargin juna da kai hare-hare.
An kashe dubban mutane a cikin shekaru da dama na rikice-rikicen ƙabila da addini masu sarƙaƙiya, galibi sun samo asali ne daga taƙaddama kan amfani da filaye tsakanin al'ummomin da galibi ke noma da kuma ƙungiyoyin makiyaya.