Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi na kawo muku abubuwan da ke faruwa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran muhimman labarai a sassan duniya na ranar 17/04/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR da Aisha Babangida

  1. Majalisar Ɗinkin Duniya ya fito da manhajar da za ta magance matsalar ƙarancin Abinci

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Babbar Darektar hukumar, Cindy McCain

    Shirin samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya, WFO ya ƙaddamar da wani shafi da ke amfani da fasahar AI, domin ganowa da kuma magance matsalar yunwa a fadin sama da kasashe 50.

    Babbar Darektar hukumar, Cindy McCain, ta ce shafin, mai suna HungerMap Live - zai rika samar da bayanai kai tsaye a lokacin da abubuwa ke faruwa, tare da bayar da hasashe, da nufin ingantawa da kuma hanzarta ayyukan samar da abinci.

    Hukumar da ke fitar da bayanai kan wuraren da aka fi fama da yunwa ta duniya, IPC, ta ce an ƙaddamar da shafin a kan gaɓa - kasancewar an yi ne a daidai lokacin da aka samu karuwar matsalar ƙarancin abinci sosai a duniya, inda aka samu alkaluman da ba a taɓa samu ba na yawan mutanen da ke fama da yunwa a shekarun nan.

  2. Ƙasashen duniya na taro kan haɗarin manhajar Claude Mythos

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministocin kuɗi da manyan jami'an manyan bankunan ƙasashe da ke halartar taron hukumar bayar da lamuni ta duniya, IMF a Washington, sun nuna fargaba a kan wata manhaja mai fasahar AI wadda kamfanin Anthropic, ya kirkiro , wadda ba a kai ga fitar da ita kasuwa ba.

    Manhajar mai suna Claude Mythos, ta nuna gagarumar kwarewa ta iya gano matsala ko yuwuwar rauni ko gazawar manhajoji.

    Ana nuna damuwa a kanta ganin yadda masu kutse da aikta miyagun laifuka ta intanet za su iya amfani da ita wajen illa ga tsaron asusun banki.

    Saboda wannan hadarin ne, kamfanin na Anthropic, ya takaita samun wannan fasaha, sai kawai ga gwamnati da wasu zababbun abokan hulda, domin bunkasa tsaron intanet.

  3. Babban jami'in ma'aikatar harkokin wajen Birtaniya zai yi murabus

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban jami'in ma'aikatar harkokin wajen Birtaniya, Olly Robbins, zai sauka daga mukaminsa bayan da ta bayyana cewa an nada Peter Mandelson a matsayin jakadan Birtaniya a Amurka, duk da cewa bai tsallake binciken jami'an tsaro ba.

    Daga baya dai an sauke Mandelson saboda alakarsa da mutumin da aka kama da laifin lalata da kananan yara, Jeffrey Epstein, kuma a yanzu yana karkashin bincike na 'yansanda.

    Shi ma Firaministan na Birtaniya na fuskantar sabon matsin lamba a kan ya sauka, bayan da aka zarge shi da yaudarar majalisa a kan maganar.

    Wakilin BBC ya ce An gaya min cewa ran firaministan ya baci sosai a kan wannan lamari

  4. An fara aiwatar da tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Lebanon

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    An fara aiwatar da yarjejeniyar dakatar da bude- wuta ta tsawon kwana goma - wadda idan an dace za ta iya kaiwa ga dakatar da yakin da aka shiga mako na shida ana gwabzawa tsakanin Isra'ila da kungiyar Hezbollah da ke Lebanon.

    Ana saran yarjejeniyar ta taimaka wajen kawo karshen yakin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran.

    Hezbollah ta ci gaba da harba makaman roka zuwa arewacin Isra'ila har zuwa lokacin da yarjejeniyar ta fara da 12 daren kasar, ita ma kuma Isra'ila an ce ta ci gaba da kai hari har tsawon rabin sa'a bayan fara yarjejeniyar.

    Isra'ilar ta ce dakarnta za su ci gaba da zama a yankuna Leabanon da suka riga suka mamaye a kudancin Lebabon.

    Hezbollah ta ce nan kuma fa daya - domin hakan ya bai wa 'yan Lebanon dama, ta tirjiya.

    Shugaba Trump wanda ya anar da yarjejeniyar - shi ne ya gayyaci jagororin kasashen biyu zuwa fadarsa ta White House domin tattaunawar.

  5. Iran ta amince ta miƙa sinadarin uranium ɗinta - Trump

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump ya nuna alamun samun kyakkyawan sakamako mai ƙarfafa gwiwa na tattaunawar zaman lafiya da Iran, inda ya ce suna dab da cimma yarjejeniyar dakatar da yaƙin.

    Ya yi ikirarin cewa Iran ta yarda ta miƙa abin da ya kira - ƙurarta ta nukiliya - yana nufin sinadarin yureniyom ɗinta wanda ta inganta - da za a iya amfani da shi wajen ƙera makaman nukiliya.

    Ya ce mun cimma matsaya da dama da Iran, kuma ina ganin wani abu zai faru ba da daɗewa ba.

    Mista Trump ya ce mai yuwuwa za a yi ganawa ta gaba da Iran ɗin a ƙarshen makon nan, kodayake ya yi gargaɗin cewa za a koma faɗa idan ba a cimma matsaya ba.

    Tun da farko jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya ce ƙasarsa na da ƙwarin gwiwa amma suna kaffa-kaffa a kan tattaunawar da Amurka.

  6. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barkan ku da warhaka a shirin shafin kai tsaye na BBC Hausa inda muke kawo muku labarai da rahotanni kan muhimman abubuwan da ke faruwa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da ƙasar Iran da abubuwan da ke faruwa a sauran ƙasashen duniya.

    Yau Juma'a kamar kullum mun dawo da shafin namu kuma da fatan za ku ci gaba da kasancewa da mu. Mun gode