'Iran ta fara jerin hare-harenta na 87 kan mafakar sojin Amurka da Isra'ila'

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) ta bayyana cewa ta fara jerin hare-haren makamai da jirage marasa matuki karo na 87 kan maɓoyar sojojin Amurka da Isra’ila da cibiyoyin su.
A cikin sanarwar da rundunar ta fitar, ta ce dakarunta sun kai hari kan “cibiyoyin kula da zirga-zirgar jiragen Amurka a UAE da wurin ma’ajin kayan makamai da moɓoyar sojojin Amurka da Isra’ila ciki har da “tsofaffin sansanonin Amurka guda biyar da kuma cibiyoyin soji a kudanci da tsakiya da arewa.”
Sanarwar ta ƙara da cewa dakarun Iran ɗin sun kai hari kan wuraren Isra'ila da suka haɗa da “Haifa Bay, da Kiryat Shmona da Tel Aviv da Beersheba da Dimona da Al-Kharj da Juffair, da kuma Victoria.”
Sanarwar ta ce "rundunar ta fara wannan jerin hare-haren ne tun farkon daren jiya kuma har yanzu yana ci gaba.”
IRGC ta bayyana cewa wannan gagarumin hari an aiwatar da shi ne da “makaman masu linzami da suka haɗa da Imad, Qiyam, da Khorramshahr 4 da kuma jiragen sama marasa matuka.






