Kwamandan Hezbollah ya mutu a wani harin da Isra'ila ta kai

Asalin hoton, Getty Images
Wani harin da Isra'ila ta kai a kudancin Lebanon ya kashe mutane huɗu ciki har da wani kwamandan ƙungiyar Hizbullah.
Ƙungiyar ta bayyana sunan kwamandan nata da Taleb Abdallah wanda ɗaya ne daga cikin manyan mayaƙan Hezbollah da aka kashe a cikin watanni takwas da suka kwashe suna gwabzawa da Isra'ila.
Kafofin yaɗa labaran ƙasar Lebanon sun ce an yi amfani da jirage marasa matuƙa a harin da aka kai a garin Joya.
Isra'ila dai ta sha alwashin ɗaukar fansar hare-haren da ƙungiyar ke kai mata a kan iyakoki, inda a baya-bayan nan wani harin da Hezbollah ta kai ya haddasa wutar daji da aka daɗe ba a kashe ba.
Ƙungiyar Lebanon a nata ɓangaren ta ce tana kai hare-haren ne kan Isra'ila da sunan martanin hare-haren kwamandojinta da Isra'ilar ke yi da kuma yaƙin da take yi a Gaza.




