Ana neman kawo mana rikici saboda batun shugabancin jam'iyya — ADC

Asalin hoton, X/ADC
Jam'iyyar adawa ta ADC a Najeriya ta yi zargin cewa wasu na neman kara jefa ta cikin rikici bayan amincewa da shugabancinta da hukumar Zaben kasar ta INEC ta yi.
Jam'iyyar ta musanta bullar wasu rahotannin da ke cewa hukumar INEC ta amince da shugabancin jam'iyyar na jihohi in da ta ce ana yunƙurin haifar da hautsini a tsakani ƴa'ƴanta.
Jam'iyyar ta ce ita ke da hakkin mika sunayen shugabanninta na jihohi ga hukumar INEC, kuma yanzu haka bata kammala aikin tattara sunayen shugabancin jihohin ba ballantana ace an amince da su.


