Kociyan tawagar Super Eagles ta Najeriya Eric Chelle ya fitar da tawagar 'yanwasa 23 da za su buga wa ƙasar wasannin neman zuwa Kofin Duniya ta 2026.
A ranar 6 da 9 ga watan Satumba Najeriya za ta buga wasa da Rwanda a gida, da kuma karawa da Afirka ta Kudu a waje.
Kocin bai kira 'yanwasan gaba ba irinsu Victor Boniface, da Sadiq Umar, da Nathan Tella. Sai kuma ɗanwasan tsakiya Yusuf Alhassan da shi ma ba zai buga wasannin ba.
Tawagar 'yanwasan ta ƙunshi:
Masu tsaron raga: Stanley Nwabali (Chippa United, South Africa); Amas Obasogie (Singida Blackstars, Tanzania); Adeleye Adebayo (Volos FC, Greece)
'Yanwasan baya: William Ekong (Al-Kholood, Saudi Arabia); Calvin Bassey (Fulham FC, England); Olaoluwa Aina (Nottingham Forest, England); Bright Osayi-Samuel (Birmingham City, England); Bruno Onyemaechi (Olympiakos, Greece); Chidozie Awaziem (Nantes FC, France); Felix Agu (Werder Bremen, Germany); Benjamin Fredericks (Dender FC, Belgium)
'Yanwasan tsakiya: Alex Iwobi (Fulham FC, England); Frank Onyeka (Brentford FC, England); Wilfred Ndidi (Besiktas FC, Turkey); Fisayo Dele-Bashiru (SS Lazio, Italy); Raphael Onyedika (Club Brugge, Belgium); Christantus Uche (Getafe CF, Spain)
'Yanwasan gaba: Ademola Lookman (Atalanta BC, Italy); Samuel Chukwueze (AC Milan, Italy); Victor Osimhen (Galatasaray FC, Turkey); Simon Moses (Paris FC, France); Cyriel Dessers (Glasgow Rangers, Scotland); Tolu Arokodare (KRC Genk, Belgium)