Harin Isra'ila ya kashe mutum 73 a arewacin Gaza

Asalin hoton, Reuters
Hukumomi a Falasɗinu sun ce aƙalla mutane 73 ne aka kashe sakamakon harin da Isra'ila ta kai a yankin Beit Lahiya da ke arewacin Gaza.
Sun bayyana cewa akwai mutane da dama da suka jikkata yayin da wasu ke maƙale a ƙarkashin ɓaraguzai.
Hotunan da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna wani bene yana ci da wuta inda aka ce wani rukunin gidaje ne da ke ɗauke da mutane da dama.
Isra'ila dai ta ce tana bincike kan rahotannin lamarin amma abin da ta gano zuwa yanzu shi ne alkaluman da Hamas ta wallafa ba gaskiya bane.
