Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 04/01/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ahmad Bawage

  1. Gwamnatin Sokoto ta bayar da bashin babura da masu ƙafa uku

    Gwamnatin jihar Sokoto ta bayar da bashin babura a farashi mai rahusa ga wasu matasan jihar domin sauƙaƙa wa al'ummar jihar.

    Mataimakin gwamnan jihar, Injiniya Idris Gobir ne ya bayyana haka lokacin bikin bayar da baburan da aka gudanar ranar Asabar a birnin Sokoto.

    Mashinan - da suka ƙunshi babura 1,000 da masu ƙafa uku su 500 - an bayar da su ne a farashi mai rahusa na ragin kashi 80 cikin 100 kan asalin farashinsu, a cewar mataimakin gwamnan.

    Injiniya Gobir ya ce shirin na daga cikin manufofin gwamnatin Sokoto na samar da ayyukan yi da sauƙaƙa wa al'umma rayuwa.

    Ya ƙara da cewa an sayi kowane babu a kan kuɗi naira miliyan 1.3 yayin da kowane mai ƙafa uku aka saye shi a kan naira miliyan 3.6, amma aka karyar da farashinsa domin taimaka wa matasan da suka amfana da tsarin.

    “Su waɗanan masu ƙafa uku mun ba ku su a kan naira miliyan ɗaya, yayain da su kuma babauran muka ba ku su a kan naira 300,000, bayan biyan kuɗin kafin-alƙalami na naira 150,000 ga kowane mai ƙafa uku, da kuma naira 50,000 ga kowane babur'', in ji mataimakin gwamnan.

    Ya ƙara da cewa waɗanda suka amfana da babura masu ƙafa uku za su riƙa biyan naira 15,000 a kowane wata, yayin da waɗanda suka karɓi babura za su riƙa biyan naira 5,000 a kowane wata.

    Haka kuma mataimakin gwamnan ya buƙaci matasan da suka amfanan su faɗaɗa tallafin zuwa ga fasinjojin da za su ɗauka da baburan nasu, ta yadda su ma al'ummar gari za su ji tallafin a jikinsu.

    “An ba ku waɗannan babura ne domin amfanin al’umma, kada ku sayar da su, kuma kada ku yi wa mutane tsada. Idan masu karɓar bashin babur ta hanyar biyan naira 90,000 a matsayin kuɗin kafin-alƙalami, na karɓar naira 100 a hannun fasinja, muna sa ran ku ku riƙa karɓar naira 20 zuwa 40, ya danganta da nisan wurin da za ku kai su'', in ji Injiniya Gobir.

  2. Girgizar ƙasa a Ethiopia ta tilasta wa fiye da mutum 20,000 barin gidajensu

    Jami'an Ethiopia sun ce sama da mutum 20,000 ashirin aka kwashe daga yankin Afar da ya fuskanci girgizar ƙasa.

    Babu wani rahoto na samun hasarar rayuka kawo yanzu.

    Gwamnatin ƙasar ta ce an tura jami'an agaji garuruwa 12 da lamarin ya shafa a yankin.

    An samu girgizar gidaje da tsagewar hanyoyin sakamakon girgizar ƙasar.

  3. 'Yanbindiga sun kashe sojojin Kamaru shida a kan iyakar Najeriya

    Jami'ai a Najeriya sun ce ƴanbindiga sun kashe sojojin Kamaru aƙalla shida a wani hari da suka kai kan iyakar ƙasashen biyu.

    Wani ɗan majalisa a yankin Akwaya da ke kudu maso yammacin Kamaru ya ce ɗaruruwan makiyaya ne suka kai hari kan wani sansanin soji.

    Wani basarake a yankin ya ce maharan sun ƙona gidansa.

    Ɗan majalisar yankin ya ce harin ramuwar gayya ne bayan sojojin Kamaru sun kashe makiyaya da dama kwana guda kafin harin.

  4. Amurka na shirin sayar wa Isra'ila makaman yaƙi na dala biliyan takwas

    Wani jami'in Amurka ya tabbatar wa BBC cewa ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta sanar wa majalisar dokokin ƙasar shirinta na sayar wa Isra'ila makamai da suka kai na dala biliyan takwas.

    Makaman - waɗanda dole sai majalisar dattawa da ta wakilai sun amince a sayar da su - sun ƙunshi makamai masu linzami da bama-bamai da sauran na'ikan harsasai.

    Matakin na zuwa ne 'yan kwanaki kaɗan kafin Joe Biden ya sauka daga muƙamin shugabancin ƙasar.

    Amurka ta yi watsi da kiraye-kirayen da ake yi mata na dakatar da bai wa Isra'ila goyon bayan soji sakamakon kashe fararen hula masu yawa a yaƙin Gaza.

    A watan Agustan shekarar da ta gabata ma Amurka ta amince da sayar wa Isra'ila makaman yaƙi da suka ƙunshi jiragen yaƙi da sauran kayan aiki na kusan dala biliyan 20.

  5. Gane Mini Hanya: Babu yarjejeniyar karɓa-karɓa a tsakanina da Atiku - Kwankwaso

    A baya-bayan nan an yi ta raɗe-raɗin cewa jagororin hamayyar Najeriya da suka haɗa da Atiku Aubakar na PDP, da Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP da kuma Peter Obi na LP na shirin dunkulewa wuri guda don tunkarar APC a zaɓen da ke tafe.

    Sai dai tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya fito fili ya nesanta kansa da rahotannin da ke cewa sun amince da yin mulki na wani wa'adi kowannesu, wato karɓa karɓa a tsakaninsu.

    Tsohon gwamnan na Kano ya kuma nuna rashin jin daɗinsa da abin da ya kira shisshigin da wasu dattawan arewacin ƙasar ke yi wajen fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa, abin da ya ce na janyo raba kan al'umma.

    A hirarsa da Imam Saleh, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya taɓo batutuwa da dama ciki har da siyasar jihar Kano, inda wasu ke ta kira ga gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsaya da kafarsa, wato ya raba gari da shi kenan, amma ya fara ne da bayyana ra'ayinsa kan dokar harajin da ta janyo cece-kuce a ƙasar.

  6. Wasu sassan Abuja za su fuskanci ɗaukewar lantarki na tsawon mako biyu

    Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki reshen babban birnin tarayya Abuja, ya ce wasu sassan birnin za su fuskanci katsewar lantarki na aƙalla makonni biyu.

    Kamfanin na AEDC ya sanar da haka ne rana Juma'a a shafinta na X, inda ta ce za a fara fuskantar rashin wutar daga ranar Litinin da ke tafe.

    Ta ce hakan zai faru ne sakamakon gyara da kuma komawa zuwa babban layin ba da wuta na megawatt 33 da kuma layin da ke bayar da wuta na megawatt 132 da ke Kukwaba.

    A cewar kamfanin, za a yi aikin komawa babban layin ne daga ranar Litinin 6 ga watan Janairu zuwa 31 ga watan.

    "Anguwannin da ɗaukewar lantarkin zai shafa sun haɗa da Lugbe da Airport Road da Kapwa da NNPC da Games Village da kuma National Stadium," in ji sanarwar da kamfanin ya fitar.

    Ya ce sauran sun haɗa da Gudu da Gbazango da sassan Kubwa da Bwari da Jahi da sassan Jabi da Karu da Nyanya da Mararaba da kuma Keffi.

  7. Kannywood ta dakatar da tauraruwa Samha Inuwa

    Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta sanar da dakatar da tauraruwa Samha Inuwa saboda zargin yin shiga mai nuna tsiraici.

    Shugaban hukumar Abba El-Mustapha shi ya tabbatar wa da BBC hakan, inda ya ce an dakatar da Samha na aƙalla tsawon shekara ɗaya.

    "Cikin abubuwan da suka sa muka da dakatar da ita har da furta kalamai marasa kyau waɗanda ba ɗabi'ar ƴan Kannywood bane," in ji El-Mustapha.

    Rahotanni sun ce hukumar ta sha yi wa tauraruwar ta Kannywood gargaɗi kan irin shiga mara kyau da kuma yin kalamai da ba su dace ba a wasu bidiyoyinta, sai dai ta bijire wa hakan kamar yadda hukumar ta yi zargi.

  8. Ƙungiyar kwallon kwando ta Miami Heat ta dakatar da ɗan wasanta Jimmy Butler

    Ƙungiyar kwallon kwando ta Miami Heat ta dakatar da ɗan wasanta Jimmy Butler na tsawon wasanni bakwai, kuma ta ce tana da niyyar sayar da shi.

    Ƙungiyar ta ce ta dakatar da shi ne bisa laifin nuna wasu ɗabi'un da suka saɓa wa dokokinta a cikin makonnin da suka gabata.

    Kwana ɗaya kafin dakatarwar, Butler - wanda ya taimaka wa Heat ta kai wasan karshe na gasar NBA har sau biyu - ya bayyan cewa ba ya ganin zai yi farin cikin ci gaba da wasa a Miami.

    Butler wanda aka sani da Buckets, zai yi asarar fiye da dala dubu ɗari uku a kowane wasa yayin dakatarwar.

  9. Lafiya Zinariya: Haɗuran da marasa lafiya ke fuskanta a yayin kulawa

    Miliyoyin mutane ne ke fuskantar cutarwa a yayin da ake kula da su a cibiyoyin kiwon lafiya, lamarin da hukumar lafiya ta ce za a iya kauce masa.

    Hukumar ta bayyana bai wa marasa lafiya kariya da cewa yanayi ne na rashin duk wani abu da zai iya cutar da su. Haka zalika matuƙar rage duk wani haɗarin da zai kai ga cutar da marasa lafiya ba da niyya ba.

    Hanya ta farko da WHO ta ce marasa lafiya na fuskantar cutarwa ita ce, ta wajen bayar da magunguna.

    Sai kura-kuran da ake samu a wajen yin tiyata.

    Wata matsalar kuma ita ce ta ɗaukar ƙwayoyin cuta, wanda hakan ke janyo daɗewa ana jinya a asibiti da janyo nakasa na dogon lokaci da kuma fuskantar matsalar bijirewa magungunan kashe ƙwayoyin cuta.

    Sai dai fiye da kashi 50 cikin ɗari na cutarwar da mara lafiya ɗaya ke fuskanta a cikin kowane mutum 20, abu ne da za a iya kaucewa.

    Don haka hukumar ta jaddada muhimmancin bayar da kariya ga marasa lafiya a lokacin da suke samun kulawa a asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya.

  10. Gwamnatin Borno za ta rage wa manoma kuɗin litar mai zuwa 600

    Gwamnatin jihar Borno ta sanar da cewa za ta rage wa manoman da suka sha fama da hare-haren Boko Haram kuɗin mai domin rage musu raɗaɗi.

    Gwamna Babagana Umara Zulum ne ya sanar da haka a ranar Juma’a a garin Bama yayin rabon tallafin kayan aikin gona ga manoma sama da 5,000 waɗanda hare-haren Boko Haram ya ɗaiɗaita.

    A cewar gwamnan, za a rage kuɗin litar mai wanda ake sayarwa kan naira 1,000 da kuma 1,200 a Maiduguri zuwa 600 ga manoman.

    "Mun yi haka ne da zimmar rage wa manoman raɗaɗi ko kuma matsalolin kuɗi da suke fuskanta, musamman ma a yankuna da aka lalata wa gine-gine da kuma wuraren kasuwanci sakamakon rikicin Boko Haram na tsawon shekaru," in ji Zulum.

    Gwamnan ya ce sun yi irin wannan hoɓɓasa a kananan hukumomin Damasak da Mobar a shekara da ta wuce, inda hakan ya sa aka samu ƙaruwar abinci da ake noma wa da kuma kyautata rayuwar mutane.

    Ya ce za su yi aiki da sojoji wajen tabbatar da cewa an kai man fetur ɗin ba tare da wata matsala ba.

    Cikin kayan da gwamnan ya raba sun haɗa da buhunan taki kirar NPK guda 2000 da kuma injunan tuka-tuka 1000.

  11. Tsohuwar kansila ta mayar da kayan banɗaki da ta cire a ofishinta bayan shan kaye a zaɓe

    Wata tsohuwar kansila a Brazil ta mayar da wasu kayayakin banɗaki da ta cire daga ofishinta bayan ta sha kaye a takararta na sake komawa kan kujerarta.

    Yanzu ta yanke shawarar ba da su ga majalisar birnin Sao Paulo.

    An sanar da matakin nata ne bayan bidiyo da hotuna na lokacin da ake tattara kayan daga ofishinta sun karaɗe shafukan intanet.

    An samu rahotannin satar kaya a ofisoshin sabbin magadan gari da wakilai a sassa daban-daban na Brazil waɗanda suka karɓi mulki a cikin makon da ya gabata.

  12. Sojojin Guatemala da El Salvador sun isa Haiti don yaƙi da ƴan bindiga

    Sojoji da dama daga Guatemala da El Salvador sun isa Haiti domin karfafa tsaro a yaƙin da ake yi da gungun masu ɗauke da makamai.

    Sojojin Guatemala 75 da kuma wasu takwas daga El Salvador sun isa ƙasar inda Firaministan Haiti Alix Didier Fils-Aimé da jakadan Amurka a Haiti Dennis Hankins suka tarbe su.

    Kenya ce ke jagorantar tawagar da Majalisar Ɗinkin Duniya ke marawa baya, wadda ta tura ‘yan sanda kusan 400 a bara, amma adadin bai kai dakaru dubu ɗayan da ta yi alƙawarin turawa ba tun da farko.

  13. Lakurawa sun kashe ƴan sanda biyu, sun yi awon gaba da shanu sama da 500 a Kebbi

    Ana ci gaba da samun bayanai game da harin da ƴan ƙungiyar nan ta Lakurawa suka kai garin Na-tisne na yankin ƙaramar hukumar Arugungun ta jihar Kebbi.

    Harin wanda suka kai a ranar Alhamis da daddare, ya janyo mutuwar ƴan sanda biyu inda kuma suka kore shanu fiye da 500.

    Sai dai an samu nasarar murƙushe maharan, a sakamakon wani ƙoƙari na haɗin gwiwar gwamnatin jihar Kebbi da jam'an tsaro.

    Shugaban ƙaramar hukumar Arugungun ta jihar Kebbi, Honarabul Aliyu Gulma ya shaida wa BBC cewa tun bayan faruwar sojoji da sauran jami'an tsaro sun bi sahun ƴan bindigar tare da kashe da dama daga cikinsu.

    "Hankali ya fara kwanciya zuwa yanzu. Ana kuma ƙoƙarin mayar da sauran dabbobi da aka ƙwato daga hannunsu," in ji Gulma.

    Ya kuma ce gwamnatin jihar ta girke jami'an tsaro da yawa a yankin tare da jan hankalin mutane wajen sanar da wuraren da suka san mayaƙan na ɓoyewa.

  14. Jaruman Kannywood da suka rasu a 2024

    Masana'antar Kannywood da masu bibiyarta na ci gaba da jimamin rasuwar fitaccen mawaƙi El'mu'az Birniwa, wanda ya rasu a daren Laraba, 4 ga Disamban 2024 a Kaduna.

    Irin yanayin da mawaƙin ya yi rasuwar fuju'a ce ta sa jimaminsa da ake yi ya ɗauki lokaci, kamar yadda ake yi idan an yi mutuwar farat-ɗaya.

    Mawaƙi El-Mu'aza ya shiga sahun irin su Saratu Daso da Mustapha Waye da darakta Aminu S. Bono wajen yin irin rasuwar ta fuju'a.

    A daidai wannan lokaci da muka yi ban-kwana da shekarar 2024, mun tattaro wasu ƴan masana'antar da suka bar duniya a shekarar.

  15. Ana daf da yanke wa Trump hukunci kan zargin biyan kuɗin toshiyar baki

    Donald Trump ya yi watsi da matakin da wani alkali a Manhattan ya ɗauka na cewa a yanke masa hukunci a ranar goma ga watan Janairu a shari’ar da aka yi masa ta biyan kuɗin toshiyar baki.

    A watan Mayu ne aka samu Mista Trump da laifi a tuhume-tuhume 34 da aka yi masa.

    Mai shari’a Merchan ya ki ya soke hukuncin da kotun ta yanke kuma ya ƙi amincewa da buƙatar yin watsi da karar – yana mai cewa zaɓaɓɓen shugaban ƙasa ba shi da kariya daga fuskantar hukunci.

  16. An koma tattaunawar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas

    Ƙungiyar Iyalan ƴan Isra'ilan da aka yi garkuwa da su a Gaza sun yi maraba da matakin da Firaminista Benjamin Netanyahu ya ɗauka na komawa tattaunawar tsagaita wuta da Hamas a Doha.

    Hamas ta ce tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan kawo karshen rikicin da kuma janyewar dakarun Isra'ila daga Gaza.

    Zuwa yanzu dai Isra'ila ta yi watsi da duk wata yarjejeniya da za ta tabbatar da kawo karshen rikicin na dindindin har sai ta cimma duka manufofinta.

  17. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barkan mu da hantsin Asabar.

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye tare da ni Ahmad Bawage.

    Ku kasance da mu domin kawo muku rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.