An kama mutum uku kan zargin hari a wurin ibadar Yahudawa a Birtaniya

Asalin hoton, Getty Images
'Yan sanda sun kama wasu mutum uku, maza biyu da mace ɗaya a matsayin waɗanda ake zargi da hannu a harin da aka kai a wani wurin ibadar Yahudawa a garin Manchester.
Hukumar tsaro ta bayyana cewa ɗaya daga cikin maharan ɗan asalin Syria ne amma yana zama a ƙasar Birtaniya inda firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya ce an harbe shi a wajen.
Firaministan ya yi kira ga ƙasar da ta tashi tsaye domin magance abin da ya kira yawaitar kyamar yahudawa yana mai jaddada buƙatar matakan gaggawa don kare al'ummomin da abin ya shafa.
Rahotanni sun bayyana cewa an kashe Yahudawa biyu yayin da uku suka samu raunuka.
Hukumar 'yan sanda da sauran jami'an tsaro suna ci gaba da bincike don gano musabbabin harin da kuma yiwuwar rawar wasu a ciki.

