MSF ta dakatar da aiki a babban birnin Haiti saboda hare-hare
Ƙungiyar bayar da agaji ta likitoci Médecins Sans Frontières (MSF) ta dakatar da ayyukanta a babban birnin ƙasar Haiti, Port-au-Prince, sakamakon wani mummunan hari da aka kai wa ma'aikatanta da kuma zargin kisan wasu majinyata biyu da ta ke zargin jami'an ƴan sandan Haiti da aikatawa.
Kungiyar agajin ta yi tir da harin a cikin wata sanarwa da ta fitar a makon da ya gabata, inda ta ce an barba wa jami’anta hayaki mai sa hawaye, kuma an tsare su ba tare da son ransu ba na tsawon sa’o’i.
Lamarin ya faru ne yayin da tashin hankali ke ƙara ta'azzara a ƙasar.
Kimanin mutane 25 ne aka kashe a birnin Port-au-Prince a ranar Talata kaɗai, a wani harin da ƴansanda suka ce artabu ne tsakaninsu da wasu ƴan daba suka yi yunƙurin kutsawa wata unguwar masu hannu da shuni.
A siyasance ma, lamarin na ci gaba da yin muni yayin da majalisar mulkin ƙasar ta kori Firaministan riƙon ƙwarya Garry Conille a wannan watan - kasa da watanni shida da hawansa mulki.