Dan takarar jam'iyyar NDC, mai hamayya a zaɓen shugaban ƙasar Ghana, John Mahama ya ce yana cike da fatan samun nasara a zaɓen da ke gudanarwa yau a ƙasar.
Yayin da yake jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan kaɗa ƙuri'arsa a mazaɓarsa ta North Tongu, John Mahama ya yaba da yadda hukumar zaɓen ƙasar ta shirya zaɓen ba tare da wata rufa-rufa ba.
''Wannan zaɓe ne da kowa zai iya hasashen abin da zai faru, saɓanin na baya da aka sha yi'', in ji shi.
John Mahama ya kuma yi fatan samun gagarumar rinjaye a majalisar dokokin ƙasar.
''Ina sa ran samun da kujerun majalisa fiye da 150'',
Ɗan takarar hamayyar ya kuma zargi gwamnatin Nana Akufo da mataimakinsa Bawumia da jefa ƙasar cikin halin matsain tattalin arziki.
''Sun lalata komai a ƙasar nan, don haka 'yan Ghana na buƙatar samun wani da zai ceto su daga halin da suke ciki.