Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi na kawo muku labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 31/01/25

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Ahmad Bawage da Aisha Aliyu Jaafar

  1. 'Za mu hukunta masu hannu a kashe farar hula lokacin mulkin Assad'

    A jawabin farko da ya yi wa ƴan kasa, aka kuma yaɗa a gidan talbijin ɗin ƙasar, shugaban gwamnatin riƙo a Syria Ahmed al-Sharaa ya yi alkawarin zai samar da ingantacciyar gwamnatin haɗaka da za ta yi tafiya da ƴan ƙasa maza da mata da kuma matasa.

    Ahmad al-Sharaa ya yi alƙawarin hukunta masu hannu a kashe-kashen farar hula a zamanin mulkin shugaba Bashar al Assad, ko da kuwa sun tsere daga ƙasar.

    A ziyarar da ya kai Syria, shugaban ƙasar Qatar Sheikh Tamim bin Hamad, ya ce ana buƙatar gaggauta samar da ingantacciyar gwamnati a Syria.

  2. Hatsarin jirgin saman Amurka: An gano bakin akwatin da ke naɗar bayanai

    An gano baƙin akwatin da ke naɗar bayanan abubuwan da suka faru a lokacin da jirgin fasinjan Amurka ya yi haɗari.

    Yanzu haka jami'ai sun dukufa domin gano abin da ya janyo jirgin ya yi taho mu-gama da wani jirgi mai saukar ungulu na sojojin Amurka a yayin da ya ke ƙokarin sauka.

    Baƙin akwatin zai taimaka wajen gano abin da ya faru a lokacin haɗarin da kuma sauƙaƙawa masu bincike aikinsu.

    An yi amanna mutum 67 da ke cikin jiragen biyu sun mutu.

    Jiragen sun yi taho mu-gama ne yayin da suke dab da sauka a filin jirgin saman Reagan da ke Washington DC.

    Mahukunta a Amurka sun ce za a kammala tattara dukkan bayanan da suka dace a game da haɗarin jiragen a cikin kwanaki 30.

    Sai dai Shugaba Trump ya ɗora alhakin haɗarin kan rikon sakainar kashi da gwamnatin Biden da ta wuce ta yi a fannin sufurin Amurka da ya sa ya lalace.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar mu barkan mu da safiyar Jumma'a.

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa.

    Ku kasance da mu domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da kuma sauran sassan duniya.