Shin za a ci gaba da tsare El-Rufai har watan Afrilu, me doka ta ce?

Asalin hoton, Kaduna State Government
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya shafe sama da kwana 10 a hannun hukumomin Najeriya.
A ranar 16 ga watan Fabarairu ne El-Rufai, bisa raɗin kansa ya je ofishin hukumar yaƙi da rashawa da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC), domin amsa gayyatar da hukumar ta yi masa.
Tun a farko hukumar EFCC ta tsare shi har zuwa daren Laraba 18 ga watan Fabrairu kafin daga baya aka miƙa shi hannun hukumar yaƙi da almundahana da dukiyar al'umma ta Najeriya (ICPC), inda tun daga wancan lokaci har yanzu ba a ƙara jin ɗuriyarsa ba.
Ko a ranar Laraba da hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya DSS ta gurfanar da tsohon gwamnan a kotu, ba a ga Malam El-Rufain ba, kasancewar hukumar ICPC ba ta kai shi kotun ba.
A ranar Laraba babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage ci gaba da sauraron karar da hukumar tsaron ta DSS ta shigar da El-Rufai game da zargin satar sauraron wayar mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro Nuhu Ribadu.
