Za mu ɗauki tsauraran matakai kan duk wanda ya karya yarjejeniya - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya yi gargaɗin cewa ƙasarsa za ta ɗauki tsauraran matakai kan duk wani ɓangare da ya karya yarjejeniyar da aka ƙulla, yana mai cewa irin wannan mataki na iya kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron yankin.
Araqchi, wanda ya kai ziyara ƙasar Iraki, ya bayyana hakan ne a yayin ganawarsa da Shugaban ƙasar, Nizar Amidi, inda ya ce karya wasu sashe-sashe na yarjejeniyar da Amurka da kuma Isra’ila suka yi musamman sashe na farko ya zama babban tarnaki ga ƙoƙarin dawo da kwanciyar hankali a yankin.
Ya ƙara da cewa Iran na ƙoƙarin aiwatar da yarjejeniyar cikin gaskiya tare da bin ƙa’idar kowane ɓangare ya cika nauyin da ya rataya a kansa.
Sai dai ya jaddada cewa Iran ba za ta lamunci duk wani saba yarjejeniyar ba, yana mai nanata cewa za su ɗauki matakan da suka dace domin kare muradun ƙasarsu da kuma tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.
Haka kuma, ya yi kira ga sauran ɓangarorin da ke cikin yarjejeniyar da su mutunta alƙawurran da suka ɗauka, yana mai cewa haɗin gwiwa da gaskiya su ne ginshikin warware rikice-rikice da ke addabar yankin Gabas ta Tsakiya.















