'Iran da Amurka za su ci gaba da tattaunawa a Doha nan da kwanaki'
Wata majiya da ke da masaniya kan tattaunawar Iran da Amurka ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Reuters cewa tawagogin ƙasashen biyu na aiki kan yadda za a ci gaba da aiwatar da tattaunawar yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Iran da Amurka kuma ana sa ran za su gana ne a birnin Doha cikin kwanaki masu zuwa.
Majiyar ta kuma bayyana cewa masu shiga tsakani sun buƙaci kafa hanyoyin sadarwa tsakanin ɓangarorin domin rage tashin hankali da kuma kauce wa duk wasu rikice-rikice, tare da ci gaba da tattaunawar fasaha a lokaci guda.
A halin yanzu, shugaban tawagar Iran, Kazem Gharibabadi, wanda ke ƙasar Oman, ya sanar da gudanar da taron farko na kwamitin hadin gwiwa kan mashigar Hormuz tsakanin ƙasashen biyu a birnin Muscat.
Rahotanni sun nuna cewa wannan yunƙuri na daga cikin matakan diflomasiyya da ake ɗauka domin rage rikici tare da tabbatar da zaman lafiya, musamman kan batun tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz, wadda ke da muhimmanci ga harkokin mai a duniya.