Wakilan Lebanon da Isra'ila za su gana da a Amurka
Wakilai daga Lebanon da Isra’ila za su gana a birnin Washington a ranar Talata, ƙarƙashin shiga tsakanin Amurka, wata guda bayan sake ɓarkewar rikici mai muni tsakanin Isra’ila da Hezbollah.
Ɓangaren Isra’ila ya ce a shirye yake ya tattauna abin da ya kira shawarwarin zaman lafiya da gwamnatin Lebanon.
Sai dai ya ce ba zai tattauna yiwuwar tsagaita wuta da ƙungiyar Hezbollah ba, tare da cewa zai nemi a kwance ɗamarar ƙungiyar.
Isra’ila na cewa hare-haren da take kaiwa a ƴan makonnin nan na shafar wuraren da Hezbollah ke da ƙarfi ne kawai, to sai dai hare-haren sama da ta kai sun kashe kusan mutane 2,000, ciki har da yara da mata da dama, da kuma likitoci da ƴan jarida da malamai.
Asibitoci sun cika maƙil sakamakon yawan waɗanda suka jikkata.
Fiye da mutum miliyan guda ne hare-haren suka raba da matsugunansu.

