Shugaban Faransa Macron ya ce ba zai lamunci ƙyamar Yahudawa ba

Asalin hoton, Getty Images
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasar ba za ta amince da ƙyamar Yahudawa ko tashin hankali ba, yayin da yake shirin halartar gasar wasan ƙwallon ƙafa tsakanin ƙasar da Isra'ila.
Aƙalla ƴansanda 4000 ne ke aikin sintiri saboda fargabar abin da zai iya biyo baya sakamakon rikicin Isra'ila a Gaza da Lebanon.
Za a fafata gasar ne mako guda bayan ƴansanda sun kama mutane da dama a Amseterdam yayin da ƴan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Ajax suka kara da takwararta ta Isra'ila Maccabi Tel Aviv.
Bayan kammala wasan, samari sun fantsama kan tituna suna kai wa magoya bayan Maccabi hari.
An zargi wasu magoya bayan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Maccabi da lalata kaya tare da yi wa Larabawa kalaman ɓatanci.


















