Al'ummar Chadi za su gudanar da zaɓen majalisar dokoki
Al'ummar ƙasar Chadi za su zaɓi 'yan majalisar dokoki a ƙasar a yau Lahadi, duk kuwa da zarge-zargen maguɗin zaɓen daga ɓagarori daban-daban.
Shugaban mulkin soji, Mahamat Idriss Deby ya ce zaɓen wani ɓangare ne na kawo ƙarshen wa'adin shirin mika mulki na shekara uku da aka yi bayan rasuwar mahaifinsa -- tsohon shugaban ƙasar.
'Yan adawa sun yi kira ga al'ummar ƙasar su ƙaurace wa zaɓen, bayan da suka yi zargin cewa Mista Deby na da niyyar yin amfani da zaɓen don ƙarfafa ikonsa.
A nata ɓangare gwamnatin ƙasar ta ce 'yan adawa na ƙoƙarin daƙile tsarin dimokradiyya ne.