Isra'ila na ci gaba da kai hare-hare a Gaza

Asalin hoton, Getty Images
Ma'aikatan lafiya a Gaza sun ce hare-hare ta sama da Isra'ila ke kai wa sun kashe mutum biyar a kudancin Zirin, tare da jikkata wasu da dama.
Waɗanda suka ga harin a sansanin 'yan gudun hijira na al-Mawasi sun ce Isra'ilar ta kai harin ne kan wani tanti.
Sannan ta biyo baya da wasu hare-haren a kusa da asibitin Kuwait, abin da ya dugunzuma iyalan da ke fake a wajen.
Hamas ta kira harin da dabbanci - na kan-mai-uwa-da-wabi, wanda kuma ya saɓa da yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta da Amurka ta samar- wadda ta fara aiki mako bakwai da ya wuce.
Rundunar sojin Isra'ilar ta ce ta kai harin ne a matsayin martani bayan da aka farmaki dakarunta.


