, Najeriya 2-0 Mozambique
An shiga cikin ƙarin lokaci na mintuna uku da aka ƙayyade.
Mozambique ta samu bugun tazara ba nisa da ragar Najeriya a gefen hagu.
Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Wannan shafi ne da zai ke kawo muku sharhi da bayanai kan wasan Najeriya da Mozambique karawar zagaye na biyu gasar kofin nahiyar Afirka 2025/26 da ake yi a Moroko.
Mohammed Abdu Mamman Skipper Tw
An shiga cikin ƙarin lokaci na mintuna uku da aka ƙayyade.
Mozambique ta samu bugun tazara ba nisa da ragar Najeriya a gefen hagu.
Geny Catamo, wanda ke kai barazana ga Najeriya, ya yi bugun tazara daga gefen dama zuwa bayan sandar raga ta nesa, inda Faizal Bangal ya taɓa kwallon da kai amma ta tafi kusa da raga amma an busa satar gida.
Bright Osayi-Samuel ya kawo kwallo daga gefen dama ta kai ga Victor Osimhen a cikin gidan Mozambique, ya sa kai, amma kwallon ta je kusa da raga amma ba ta shiga ba.
Mai tsaron ragar Mozambique, Ernan, ya ji rauni yayin da yake ƙoƙarin dakatar da wƙwallon.
Alex Iwobi ya sake bayar da ƙwallo daga layin rabin fili a gefen hagu, inda ya buga kwallo ba tare da kallon ba zuwa ga Ademola Lookman a gabansa, daga kusa da da'ira.
Akor Adams ya taɓa kwallon a hankali daga bugun da Lookman ya yi a cikin gidan Mozambique, sai ya bai wa Victor Osimhen wanda ba a san yana wajen ba, sai ya ci ƙwallon cikin sauki.
Mai Afcon uku ta fara samun natsuwa a wasan.
Najeriya sai kara kai hare-hare take ta san ƙwallo ɗaya ba abin dogara bace, kuma tun kafin wasan ya yi nisa take son kammala shi
Alex Iwobi ya ɗaga kai sannaun ya buga wa Ademola Lookman shi kuma bai ɓata lokaci ba ya zura a raga.
Reinildo ya samu bugun kusurwa, Mozambique ta buga ƙwallon da ƙarfi daga bugun kusurwar, ta fitar zuwa jifa ga Najeriya.
Najeriya ta samu bugun tazara ba nisa da bakin ragar Mozambique a gefen hagu.
Ademola Lookman ya daga hannu yana kiran ‘yan wasansa da ke cikin da'ira ta 18 domin su shirya karɓar kwallon.
Victor Osimhen, ya na wasan daren yau ba tare da abin rufe fuska na kariya ba.
Wannan abin kariyar fuska mai launin baki da aka ƙera masa na musamman ya zama koda yaushe ɗan wasan mai shekaru 27 na amfani da shi, tun bayan dawowarsa fili daga raunin fuska da ya samu a watan Nuwamba 2021.
Wannan rauni na daga cikin dalilan da ya sa ya rasa halartar gasar AFCON 2021 da aka gudanar a Kamaru
Yanzu dai ya cire abin kariyar, Osimhen na kokarin ganin ya zura ƙwallo a wasan da ake yi a Fes.
An fara samun nutsuwa a wasan bayan an soke kwallon da Victor Osimhen ya zura a raga.
Najeriya na ci gaba da taka rawar gani tare da neman hanyoyin damar cin ƙwallo.
Jim kaɗan bayan mai tsaron ragar Mozambique, Ernan, ya kama wata kwallo da Bright Osayi-Samuel na Birmingham City ya buga daga gefe, Najeriya ta kuma amfana, inda Frank Onyeka na Brentford ya bai Victor Osimhen ƙwallon.
Shi kuwa ɗan wasan gaba ya zura kwallon da kai, amma nan take aka daga tutar satar gida.
An samu ɗan jinkiri a wasan yayin da wani daga cikin ma’aikatan filin wasa ke gyara wani ɓangare na ragar kwallo.
‘Yan wasa kuma suna watsawa da buga kwallo domin su ci gaba da kasancewa cikin ɗumi.
Ana kuma ruwa a filin ko ina ya jike.
Najeriya na fatan lashe Afcon na huɗu a bana a Morocco, za kuma ta ƙara da Mozambique a wasan zagaye na biyu ranar Litinin a Stade de Fes.
Wannan shi ne karo na biyu da za su kece raini a gasar cin kofin Afirka.
Sun fara haɗuwa a karawar cikin rukuni a 2010, inda Najeriya ta yi nasara 3-0
Jimilla sau biyar suka fafata a tsakaninsu, Najeriya ta yi nasara huɗu da canjaras ɗaya.
Wasan baya-bayan nan da suka haɗu shi ne a sada zumunta da suka yi ranar 16 ga watan Oktoban 2023 a Portugal, Najeriya ce ta yi nasara 3-2.
Har zuwa Lahadi, 28 ga watan Disamba, ƙasar Mozambique ba ta taɓa samun nasara ba a gasar cin kofin nahiyar Afirka.
Wasa 16 ta yi kuma tsawon shekaru masu yawa, sun wuce ba tare da ta yi murnar cin wasa ba a tarihin babbar gasar ta Afirka.
Wannan dogon jira ya zo ƙarshe a Grand Stade d’Agadir, inda Mambas suka ba kowa mamaki ta hanyar doke Gabon da ci 3–2, ɗaya daga tarihin da ba za a manta da shi ba.
Wannan sakamako ya zama tarihi a fani biyu: ya zama nasara ta farko a tarihin Mozambique a AFCON, sannan kuma ya tabbatar da karon farko da ta tsallaka zuwa zagayen ziri ɗaya ƙwale, duk da cewa wannan ne karo na shida kacal da suke halartar gasar Afcon.