Mutum 44 sun ɓace bayan motar fasinja ta faɗa kogi a Jamhuriyar Benin
Ana ci gaba da aikin gano mutane 44 da suka ɓace bayan wata motar bas ta faɗa cikin kogin Ouémé da ke tsakiyar ƙasar Jamhuriyar Benin.
Motar mai ɗauke da fasinjoji 54 ta taso ne daga birnin Lomé na ƙasar Togo zuwa birnin Yamai na jamhuriyar Nijar a lokacin da ta faɗo daga saman wata gada.
Yawancin fasinjojin ƴan ƙasashen Benin da Nijar ne.
RAhotanni dai sun bayyana cewa fasinjoji 9 ne suka tsallake rijiya da baya inda aka gano gawar mutum ɗaya, sannan 44 suka ɓata.
A cikin wata sanarwa, shugaban ƙasar Benin, Patrice Talon, ya bayyana alhininsa tare da miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan da bala'in ya shafa.
Ya kuma jaddada muhimmancin ƙarfafa matakan kiyaye hanyoyin ƙasar don hana afkuwar irin wannan mummunan lamari nan gaba.
Shugaban ya kuma buƙaci kamfanonin sufuri da direbobi da su kiyaye dokokin ahnay tare da sanar da matakan da gwamnati za ta ɗauka na inganta bincike don tabbatar da lafiyar ababen hawa da kuma tilasta tsauraran mataka a kan titunan ƙasar.



















