Fararen hula sun maƙale a birnin El-Fasher da RSF ta mamaye

Asalin hoton, Getty Images
Fargaba na ci gaba da karuwa a kasar Sudan, sakamakon daruruwan fararen hula ne suka kasa ficewa daga birnin El-Fasher bayan da dakarun RSF suka bayyana iko da birnin.
Kungiyar bayar da agajin ta ce dubban mutane ne suka isa Tawilla a cikin dare, inda galibinsu suka makale a El Fasher, birnin da ya kwashe lokaci yana fuskantar hare-haren dakarun sojin Sudan da na RSF.
Kungiyar bayar da agaji ta Medicine San Frontiers, ta yi gargadin cewa za a iya samun kisan iyashi idan har ba a ba jama'a damar fita daga birnin ba.
Ta ce gwamman mutanen da suka samu rauni sun samu isa garin Tawilla mai nisan kilomita shida yamma da birnin.













