Ban tuntuɓi Iran don tattaunawar zaman lafiya ba - Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya wallafa a dandalin sa na Truth Social cewa bai tuntubar Iran don tattaunawar zaman lafiya "ta kowace hanya ko tsari ko salo" ba.
Trump ya ƙara da cewa Iran ya kamata a ce ta sa hannu a yarjejeniyar da ya gabatar a lokacin da aka yi taron karshe kan shirin nukiliyar ƙasar.
Trump ya ce, “Wannan wani labari ne na ƙarya da aka ƙirƙira, Idan suna son tattaunawa, sun san yadda za su same ni. Ya kamata a ce sun amince da yarjejeniyar da aka gabatar musu — hakan da ya ceci rayuka da dama”.







