Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya. 25/11/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Ahmad Bawage da Isiyaku Muhammed

  1. Mutane 16 sun ɓace bayan nutsewar jirgin ruwa a tekun Bahar Maliya

    Hukumomi a ƙasar Masar sun ce mutane 16 sun ɓace, ciki har da ƴan kasashen waje, sannan an ceto 28 bayan wani jirgin ruwan ƴan yawon buɗe ido ya nutse a tekun Bahar Maliya.

    Biyu daga cikin waɗanda suka ɓata ƴan Burtaniya ne, kamar yadda BBC ta fahimta.

    Ƙasar Finland ta tabbatar da cewa ba a ga ɗaya daga cikin ƴan kasarta ba, yayin da hukumomi suka ce ƴan ƙasar Masar huɗu ma sun ɓace.

    Hukumomin kasar ba su bayyana dalilin da ya haddasa nutserwar jirgin mai ɗauke da mutane 44 ba, sai dai bayanai daga waɗanda suka tsira sun nuna cewa igiyar ruwa ce ta afkawa jirgin da ya yi sanadin kifewarsa.

    Masu hasashen yanayi sun yi gargadi game da tafiya kan teku a ranar Lahadi da Litinin.

    Jirgin mai suna 'Sea Story' ya bar tashar jiragen ruwa kusa da Marsa Alam ranar Lahadi don balaguron na kwanaki biyar, a cewar jami'ai.

    Gwamnan yankin Manjo-Janar Amr Hanafi ya ce an gano waɗanda suka tsira ne a yankin Wadi el-Gemal da ke kudancin Marsa Alam, kuma suna samun kulawar da ta dace a asibiti.

  2. Ambaliya ta mamaye wasu yankunan Burtaniya

    Ana ci gaba da fama da matsalar ambaliyar ruwa bayan mamakon ruwan sama da aka fuskanta a wasu sassan Burtaniya a ƙarshen mako, wanda ya yi sanadiyar lalacewan gidaje, da tituna da kuma layukan dogo.

    Aƙalla mutane uku ne suka mutu kuma lamarin ya haifar da suka game da rashin shiri da rashin gargaɗin mutane game da tsananin yanayin da za a iya fuskanta.

    An sanar da wani babban lamarin agajin gaggawa a yankin Northamptonshire, wuri ɗaya tilo da har yanzu ke fuskantar barazanar sake samun mummunan ambaliyar ruwa, bayan wani wurin shakatawa ya nutse a karo na uku a wannan shekara.

    Ƴan siyasa da mazauna yankin kudancin Wales, daya daga cikin yankunan da ambaliyar ta fi Ƙamari, sun soki abin da suka kira rashin shiri da kuma rashin isasshen gargadi daga jami'ai.

    Ƴan sanda a yankin suna gargadi game da duk tafiye-tafiyen da ba su zame dole ba, kuma sun shaida wa mutane ka da su tuƙa mota a cikin ruwa ko da kuwa ba shi da zurfi.

  3. Ana ci gaba da musayar wuta tsakanin Rasha da Ukraine

    Rasha da Ukraine sun ci gaba da musayar hare-hare ta sama, bayan shafe mako guda ana cacar baki tsakanin ƙasashen inda Rasha ta gwada wani sabon makami mai linzami kan Ukraine.

    Rasha ta kai aƙalla hare-hare 1,500 kan Ukraine tun daga yammacin ranar Lahadi a kusan rabin yankunan ƙasar wanda ya yi sanadin jikkatar mutane da dama, in ji shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky.

    A halin da ake ciki kuma sojojin Ukraine sun ce sun kai hari a wani muhimmin ma'ajiyar mai a kudancin birnin Moscow, da kuma yankunan da ke kan iyakar Bryansk da Kursk.

    Amfani da makami mai linzami na Oreshnik da Rasha ta yi a kan birnin Dnipro na ƙasar Ukraine ya ƙara rura wutar yaƙin inda Ukraine ta harba makamai masu linzami na Amurka da Birtaniya zuwa cikin Rasha a karon farko.

    An rawaito cewa shugaban Amurka Joe Biden ya bai wa Ukraine izinin yin amfani da makamai masu linzami masu cin dogon zango cikin Rasha ne a matsayin martani kan amfani da sojojin Koriya ta Arewa da Moscow ke yi.

    Gwamnan Kharkiv Oleh Synehubov ya ce mutane 23 ne suka jikkata sakamakon harin makami mai linzami da aka kai a birnin Kharkiv, inda a yanzu haka ake ci gaba da gudanar da aikin ceto.

  4. Ban yi mamakin jin wasu na son a sake zaɓe ba - Starmer

    Firaministan Birtaniya Sir Keir Starmer ya ce bai yi mamakin jin cewa wasu da ba su zaɓi jam'iyyar Labour ba a zaɓen da ya gabata ke son a sake gudanar da zaben.

    Wani ƙudurin koke a shafin intanet na majalisar dokokin ƙasar da ya zargi jam'iyyar Labour da saɓa alƙawari da kuma kiran da a gudanar da sabon zaɓe ya tattara sa hannun sama da mutane miliyan biyu - wanda shi ne na uku mafi girma tun shekara ta 2010.

    Ƙudurin ya samu sa hannun sama da mutane 100,000, don haka akwai yiwuwar a yi muhawara kan batun a majalisar, amma ba zai haifar da sabon zaɓe ba.

    Da aka tambaye shi game da ƙudurin a shirin 'This Morning' a gidan talabijin na ITV, Sir Keir ya ce: "Za a sami ɗimbin mutanen da ba sa son mu tun farko...hankali kaabin da na fi mayar da hankali a kai shi ne abubuwan da zan zartar kowace rana."

    Firaministan ya ce ya gaji matsaloli da dam daga gwamnatin da ta gabata kuma ya yanke shawarar "daukar tsauraran matakai tun tashin farko".

    Ƴan Birtaniyya da mazauna ƙasar na iya wallafa takardar koke a shafin intanet na gwamnatin Birtaniya ko majalisar dokoki.

    Korafe-korafen da suka samu sa hannun sama da mutane10,000 za su samu amsa daga gwamnati sannan waɗanda suka tattara sunaye sama da 100,000 za a yi muhawara a kansu a zauren majalisar.

  5. An kama mutane uku bisa zargin kashe bayahude a UAE

    Hukumomi a Hadaɗɗiyar Daular Larabawa sun ce sun gano wasu ƴan ƙasar Uzbekistan su uku a matsayin waɗanda ake zargi da kisan wani malamin addinin yahudawa ɗan asalin ƙasar Maldova, inda suka ce suna ƙoƙarin gano dalilin da ya haddasa aikata kisan.

    Ma'aikatar harkokin cikin gida ta buga hotunan wasu mutane uku da suka rufe idanuwansu waɗanda ta bayyana sunayensu da Olimboy Tohirovich da Makhmudjon Abdurakhim da Azizbek Kamilovich.

    An gano gawar Rabbi Zvi Kogan, mai shekara 28, wanda ma’aikaci ne na ƙungiyar Yahudawa ta Chabad Lubavitch a Abu Dhabi, ranar Lahadi, kwanaki uku bayan ya bace.

    Isra'ila ta yi alla-wadai da kisan a matsayin "harin ta'addanci na ƙyamar Yahudawa" tare da yin alƙawarin zaƙulo waɗanda ke da hannu a ciki. Moldova kuma ta kira lamarin "zallan ƙyamar yahudawa".

    Jakadan Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa a Amurka ya ce laifi ne aka yi wa kasar Larabawa ta yankin Gulf, wadda ta ƙulla cikakkiyar hulɗar diflomasiyya da kasuwanci da Isra’ila a shekarar 2020.

    A yammacin yau litinin ne ake sa ran za a yi jana'izar Rabbi Kogan a birnin Ƙudus, bayan da wata ƙungiyar yahudawa da ke tattara gawarwakin mamata domin binne su, ta ce jirgin da ke ɗauke da gawarsa ya tashi daga Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

  6. Isra'ila da Lebanon sun kusa cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

    Jami'an Isra'ila da Amurka sun bayyana cewa akwai alamun Isra'ila da Lebanon sun kusa cimma yarjejeniyar tsagaita wuta, inda majalisar ministocin Isra'ila za ta yi taro ranar Talata domin tattaunawa kan batun.

    Ana shirin tsagaita wuta na kwanaki 60 domin kawo ƙarshen faɗa tsakanin Isra'ila da ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon da ke samun goyon bayan Iran.

    An ce yarjejeniyar za ta ƙunshi batun janyewar sojojin Isra'ila daga kudancin Lebanon da kuma kawo ƙarshen kasancewar ƙungiyar Hezbollah a yankin.

    A dai halin yanzu ana ci gaba da samun musayar wuta tsakanin Isra'ila da Hezbollah, a daidai lokacin da bangarorin biyu ke ta kai-komo kan bayanan da ke ƙunshe cikin yarjejeniyar.

    A ranar Lahadin da ta gabata an harba makamai masu linzami 250 zuwa Isra'ila daga Lebanon, inda aka kakkaɓo akasarinsu, yayin da sojojin saman Isra'ila ke ci gaba da kai hare-hare ta sama kan wuraren da ake zargin ƙungiyar Hezbollah ajiye makamai a Beirut da sauran wurare.

    Yarjejeniyar dai za ta haɗa da ƙara yawan sojojin ƙasar Lebanon a yankin da Isra'ila da Hezbollah suka janye a cewar wani jami'in diflomasiyyar ƙasashen yammacin duniya da ya nemi a sakaya sunansa.

    Hukumomin ƙasar Labanon sun ce duk wata yarjejeniyar tsagaita wuta ya kamata kasance kan sharuɗɗan ƙuduri mai lamba 1701 na Majalisar Dinkin Duniya, wanda ya kawo ƙarshen yaƙin shekarar 2006 tsakanin Hezbollah da Isra'ila.

  7. An kama wani mutum bayan ya harbe yarinya ƴar shekara takwas a mota

    An kama wani matashi ɗan shekara 22 bisa zargin yunƙurin kisan kai bayan harbin wata mota har sau biyu wanda ya yi sanadin jikkata wata yarinya ƴar shekara takwas da mahaifinta.

    An kai su asibiti sakamakon harbin da aka yi a Kudancin Row a Ladbroke Grove a birnin Landan ranar Lahadi, kuma suna ci gaba da kasancewa cikin mawuyacin hali, in ji rundunar ƴan sandan birnin.

    Duka waɗanda harin ya rutsa da su sun samu "mummunan raunukan harbin bindiga". Yarinyar a halin yanzu tana aikin tiyata yayin da mahaifinta, mai shekaru 34, ya samu raunukan da za su iya sauya rayuwansa.

    Supt Owen Renowden ya shaida wa manema labarai cewa, yayanta ɗan shekara biyu da mahaifiyarsu, mai shekaru 32, suna cikin motar amma "ba su fuskanci wata matsala ba."

    Ya ƙara da cewa bincike na ci gaba da gudana cikin gaggawa, kuma yana so ya ji ta bakin duk wanda ke da labarin abin da ya faru

  8. Ƴan ci-rani takwas ciki har da yara sun nitse a tekun Girka

    An gano gawawwakin mutane takwas da suka haɗa da kananan yara shida bayan da wani kwale-kwalen ƴan ci-rani ya nitse a tsibirin Samos na ƙasar Girka, kamar yadda hukumar tsaron gaɓar ruwan kasar ta sanar.

    Kimanin mutane 40 ne hukumomi suka ceto yayin wani samame da suka kai a tekun Aegean, in ji hukumomi.

    Iska mai karfi na janyo tsaiko a ayyukan ceto.

    Wani jami'i ya ce wata ƙungiya mai zaman kanta ta sanar da hukumomi halin da ake ciki, kuma ana kyautata zaton mutane kusan 50 ne ke cikin jirgin.

    Samos dai yana kusa da gaɓar tekun Turkiyya kuma ya daɗe da zama wurin da bakin haure suka saba bi domin isa ƙasashen Turai.

    Fiye da ƴan ci-rani 50,000 ne suka isa ƙasar ta Girka ta ruwa a bana, wanda ya zama hanya ta biyu da aka fi amfani da ita wajen zuwa Turai - inda Italiya ke gaba.

    Ƴan ci-rani da ke shiga Turai na raguwa tun watan Agustan 2023, amma sun sake ƙaruwa tun lokacin bazara, a cewar bayanai daga hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya, UNHCR.

    Kimanin ƴan ci-rani 160,000 ne suka isa Turai ta teku a bana, kamar yadda alkaluman hukumar suka nuna, yayin da mutane 2,000 suka mutu ko kuma suka ɓace.

    Kusan kashi 23 na masu shiga Turai ɗin sun kasance yara.

  9. Tsohon malamin tarihi ya lashe zaɓen Uruguay

    Wani tsohon malamin tarihi mai ra'ayin kawo sauyi, Yamandú Orsi, ya lashe zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a Uruguay.

    Orsi ya doke Álvaro Delgado ɗan takarar jam'iyyar masu ra'ayin mazan jiya da fiye da kashi uku cikin 100 a zagaye na biyu na zaɓen na ranar Lahadi.

    Delgado ya amince da shan kaye, ya kuma taya Orsi da gamayyar jam'iyyunsa ta Broad Front murna, waɗanda a yanzu za su koma kan karagar mulki bayan shekaru biyar na mulkin ƴan mazan jiya.

    Broad Front dai ta mulki Uruguay na tsawon shekaru 15 daga 2005 zuwa 2020 kafin daga bisani shugaba mai barin gado Luis Lacalle Pou ya yi nasara- wanda a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin Uruguay aka hana shi tsayawa takara karo na biyu a jere a wannan zaɓe.

    Ana kallon Orsi mai shekaru 57 a matsayin ɗan gaban goshin tsohon shugaban ƙasar José Mujica, wanda ya samu karɓuwa a zukatan mutane da dama a ƙasar ta Uruguay sakamakon salon rayuwarsa, lamarin da ya sa mutane da dama ke yi masa laƙabi da "shugaban da ya fi talauci a duniya".

    Orsi ya girma ne a ƙauyen Uruguay a cikin gidan da babu wutar lantarki.

    Yayin da yake aiki a matsayin malamin tarihi a makaranta, ya zama mai himma a harkokin siyasa na cikin gida, daga ƙarshe ya zama magajin garin Canelones, yankin na biyu mafi yawan jama'a na Uruguay.

  10. Dubban magoya bayan Imran Khan na ci gaba da tattaki a babban birnin Pakistan

    Babban birnin Pakistan, Islamabad, na fuskantar hana zirga-zirga a rana ta biyu a yayin da dubban masu zanga-zangar neman a sako tsohon Firaminista Imran Khan daga gidan yari suka yi dafifi a birnin.

    Magoya bayansa suna kuma yin kira da a soke sakamakon zaɓen da suka ce an tafka maguɗi - iƙirarin da gwamnatin ƙasar ta musanta.

    Tsohon Firaministan dai ya shafe sama da shekara guda ana tsare da shi bisa tuhume-tuhume daban-daban, amma ya kasance mai farin jini sosai duk da matsalolin shari'a da ya ke fuskanta kuma magoya bayansa sun shafe watanni suna zanga-zanga.

    Matar sa Bushra Bibi ta shaidawa magoya bayanta a ranar litinin cewa za a ci gaba da gudanar da tattakin har sai mijin nata ya samu ƴanci.

    Gangami na baya-bayan nan ya zo ne bayan da Khan ya yi kira ga magoya banaynsa su ci gaba da zama a babban birnin ƙasar har sai an biya musu bukatunsu.

    An yi arangama tsakanin magoya bayansa da ƴan sanda.

    Hukumomin ƙasar sun haramta zanga-zangar, tare da toshe tituna da kuma dakatar da intanet.

    Makarantu da kwalejoji sun kasance a rufe saboda fargabar ɓarkewar tashin hankali.

  11. Ƴansanda sun daƙile harin ƴanbindiga a Katsina

    Rundunar ƴan sandan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta ce ta daƙile wani harin ƴan ta’adda a ƙaramar hukumar Jibia da ke jihar, tare da ceto mutane da dama.

    Lamarin ya faru ne bayan ƴanta’addan ɗauke da muggan makamai sun kai hari kan wasu motoci biyu ɗauke da fasinjoji a ƙauyen Ɗan’arau da ke Magama Jibia a jihar ta Katsina.

  12. Jagoran NNPP na jihar Borno ya ajiye muƙaminsa

    Jagoran jam'iyyar NNPP na jihar Borno, Attom Muhammad Magira ya ajiye muƙaminsa na jagorancin jam'iyyar, da ma jagorancin ƙungiyar Kwankwasiyya ta jihar.

    A wata wasiƙa da ya rubuta zuwa shugaban jam’iyyar NNPP na mazaɓarsa ta Gwanje I, Magira ya ce, “ni Attom Muhammad Magira na ajiye muƙamin jagoran jam’iyyar NNPP a jihar nan da kuma ƙungiyar Kwankwasiyya movement a jihar Borno daga ranar 25 ga Nuwamban 2024.

    "Ina godiya da goyon bayan da mutanen Borno suka ba ni, kuma ina godiya da goyon bayan da na samu daga babban madugun NNPP, Injniya Rabiu Musa Kwanwaso."

  13. Ya kamata a yanke wa Netanyahu hukucin kisa - Khamenei

    Jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce hukuncin kisa ya kamata a yanke wa firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, maimakon sammacin kama shi da kotun hukunta manyan laifuka ta yi.

    Kotun ta zargi Mista Natenyahu da tsohon ministan tsaron ƙasar da aikata laifukan yaƙi a Gaza.

    Tuni firaiministan ya bayyana sammacin da ƙiyayya ga Yahudawa.

    A ranar Lahadi, ɗaya daga cikin manyan hadiman Ayotallahi (Ali Larijani) ya ce Iran na shirye-shiryen mayar da martanin hare-haren Isra'ila a ƙasar.

  14. Rikici kan mallakar masallaci ya haifar da kisan mutum huɗu a Indiya

    Mutanen yankin arewacin birnin Sambhal sun wayi gari da firgici bayan mutum huɗu sun rasu, sannan wasu gommai sun jikkata a wani rikici da ya ɓarke kan mallakar wani tsohon masallacin jihar a ranar Lahadi.

    Rikicin ya ɓarke a tsakanin masu zanga-zanga da ƴansanda a lokacin da ake gudanar da wani bincike, wanda wata kotu ta sa a yi a game da masallacin na Shahi Jama Masjid, wanda masallaci ne da yake gine tun a ƙarni na 16, wanda yanzu gwamnati ta mayar wajen tarihi mai muhimmanci na ƙasar.

    Hukumomi a jihar Uttar Predash - inda birnin Sambhal yake - sun shigar da ƙararraki guda huɗu kan rikicin, kuma sun dakatar da intanet tare da rufe makarantun yankin na kwana ɗaya.

    Wata kotu ce ta bayar da umarnin gudanar da binciken a makon jiya, jim kaɗan bayan an kai mata ƙara cewa an gina masallacin ne a filin wani tsohon wajen bauta da aka rusa.

    Bidiyo da hotunan da aka yaɗa na rikicin sun nuna takalma da duwatsu da aka riƙa yin jifa da su a kusa da masallacin.

    Masu zanga-zangar sun yi zargin cewa ƴansanda sun harbi mutum huɗu, amma hukumomi sun musanta zargin.

    "Ba a yi amfani da makamin da zai iya kashe mutum ba," in ji Krishan Kumar, wanda sufuritandan ƴansanda ne a zantawarsa da jaridar Hindu.

    Wannan rikicin na masallacin Shahi Jama na cikin rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar a game da masallatai, inda ƙungiyoyin Hindu suke ikirarin cewa mahukuntan Mughal sun rusa wuraren ibadarsu domin gina masallatai.

    Ƙungiyoyin musulmi da dama na cigaba da fama da shari'o'i a game da koken a kotuna.

  15. Tattalin arziƙin Najeriya ya bunƙasa - NBS

    Hukumar ƙididdiga ta ƙasa, wato NBS, ta ce tattalin arzikin Najeriya ya bunƙasa da kashi 3.46 a rubu'i na uku na wannan shekarar ta 2024.

    Wannan nasarar ta samu ne a cikin sauri idan aka kwatanta da rubu'i biyu na farko a shekarar ta 2024, kamar yadda rahoton NBS ya nuna.

    Sai dai duk da bunƙasar ta tattazlin arzikin, wato kashi 3.19 a rubu'i na biyu, da 2.98 a rubu'i na farko, har yanzu ba a kai ga samun nasarar bunƙasa tattalin arzikin ƙasar da kashi 6 ba kamar yadda gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta yi alƙawari.

    Nasarar da aka samu ba ta rasa nasaba da ci gaban da aka samu a ɓangaren harkokin tattalin arziki da suka shafi bankuna da intanet, wanda ya inganta tattalin arzikin ƙasar da kashi 50 a tsakanin Yuli da Satumba.

    Wasu matakan da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ɗauka a makonsa na farko a mulki sun sa an yi tunanin zai bunƙasa tare da inganta tattalin arzikin ƙasar, wada ita ce mafi girman tattalin arzikin nahiyar.

    Amma bayan wata 18 da fara mulkin, manyan matakan da ya ɗauka - cire tallafin man fetur da karya darajar naira - sun jawo tsadar rayuwa da aka daɗe ba a gani ba a ƙasar a cikin shekaru masu yawa, amma har yanzu ba a fara gani a ƙasa ba.

    Ɓangaren man fetur na ƙasar, wanda shi ne kan gaba wajen samar da kuɗin shiga ga gwamnatin ƙasar, ya samu bunƙasa da kashi 5.17, inda gangar man da ake fitarwa a ƙasar ya ƙaru zuwa ganga miliyan 1.47 a rana, maimakon ganga miliyan 1.41 da ake fitarwa a rubu'i na biyu na shekarar.

    An samu koma-baya ne a ɓangaren noma daga kashi 1.41 a rubu'i na biyu, zuwa 1.14 a rubu'i na ukun, sannan ɓangaren masana'antu ya samu tagomashi daga 2.18 zuwa 3.35 a watan Afrilu zuwa Yuni.

    Bankin bayar da lamuni ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka da kashi 2.9 a shekarar 2024, da kuma 3.2 a shekara mai zuwa.

  16. Zulum ya raba tireloli 100 na hatsin da Tinubu ya ba Borno

    Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya raba tireloli 10 na kayan abinci da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ba jihar gudunmuwa.

    Gwamna ya ƙaddamar da rabon ne a ranar Litinin a wasu cibiyoyi ga mazauna Gambarou da Ngala da sauran garuruwa, inda aka samu tsaikon abinci a sanadiyar ambaliyar ruwa da ta ɗaiɗaita babban birnin jihar.

    Kayan hatsin sun ƙunshi masara da gero da dawa, kuma an raba ga iyalai ne, musamman ga waɗanda suka fi fama da rashin abinci.

    Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan ƙaddamar da raba abincin, Zulum ya ce an zaɓi Ngala ne, "saboda sai da ambaliyar ta raba garin baki ɗaya daga sauran ɓangarorin jihar na kusan wata huɗu. Wannan ya sa muko zo nan a yau domin ƙaddamar da rabon abincin nan domin rage wa mutanen yankin raɗaɗin da suka shiga."

    Zulum ya yaba wa shugaban ƙasa Bola Tinubu da sauran hukumomin gwamnatin tarayya bisa goyon bayan da suka ba jihar.

    "Dukkan abinci da muka raba a yau, shugaban ƙasa Bola Tinubu ne ya ba mu. Muna godiya ga gwamnatin tarayya bisa wannan goyon baya.

  17. Tsohon hadimin Buhari ya gargaɗi Tinubu kan amfani da shawarwarin IMF

    Tsohon shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa na tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, farfesa Ibrahim Gambari, ya gargaɗi gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta su riƙa yin taka-tsantsan wajen amfani da shawarwarin bankin duniya da bankin lamuni na duniya wato IMF.

    Gambari ya ce, "mene ne amfanin tsare-tsaren gwamnati idan mutane ba sa so?" in ji shi a tattaunawarsa da tashar Channels.

    "Bankin duniya da IMF abokan hulɗarmu ne, don haka idan suka kawo mana wasu shawarwari, sai muka ga ba za su ɓille mana ba, sai mu gyara su domin su dace da tsarinmu, saboda jin daɗin mutanenmu da ci gaban ƙasarmu ne a gaba da komai."

    Farfesa Gambari ya ƙara da cewa Najeriya ta ci sa'a, "saboda da wasu ƙasashen ne rayuwa ta yi tsada haka, da zanga-zanga ce za ta ɓarke. Ƴan Najeriya ba sa damuwa kan neman abubuwa masu yawa daga gwamnati, shi ya sa kowa ya cigaba da gudanar da harkokinsa. A ƙasashe irin su Sudan, farashin burodi ne ya ƙaru da kashi 20, amma zanga-zange ta ɓarke wanda ta rikiɗe zuwa tarzoma. Amma a Najeriya mutane suna gyara zama ne kawai su cigaba da harkokinsu. Amma ya kamata mu ɗauki matakin da ya dace, ba sai an yi juyin juya hali ba."

  18. An gudanar da taron Katsinawa da Gobirawa a Nijar

    A jamhuriyar Nijar wata ƙungiyar ci gaban birni da karkara a jihar Maraɗi ce ta gudanar da wani babban taro wanda ya bada damar tattauna batun haɗin kan al'umma jihar musaman Katsinawa da Gobirawa.

    Hakan dai na daga cikin burin hukumomin ƙasar, kamar yadda suke cewa na haɗa kan al'umma da tabbatar da kwaciyar hankali da zaman lafiya da kuma kyautata zamantakewa tsakanin al'ummomin.

  19. Sojojin Nijar sun kashe Lakurawa a kan iyakar Najeriya

    Rundunar sojin Jamhuriyar Nijar ta bayyana cewa jami'anta sun kashe ƴan Lakurawa - waɗanda suka shiga ƙasar ta kudu maso yammaci, kamar yadda kafar Tamtan.info mai zaman kanta ta ruwaito a ranar 25 ga Nuwamba.

    Rundunar ta ce sun kashe mayaƙan ƙungiyar a ranar 21 ga Nuwamba a Muntseka, na yankin Illela da ke kudu maso yammacin jihar Tahoua da ke kan iyakar ƙasa da Najeriya.

    Rahoton ya ƙara da cewa, "ƴan ta'adda ne da ake kira Lakurawa ko Lukurawa da suka ɓulla a jihohin arewa maso yammacin Najeriya musamman, Kebbi da Sokoto da suke da iyaka da jihohin Jamhuriyar Nijar wato Dosso da Tahoua, inda suka kashe mutum 15.

    "Wataƙila sun gudu ne daga Najeriya suka shiga Nijar domin tserewa daga yaƙarsu da sojojin Najeriya ke yi," in ji rahoton.

    Lakurawa sun ɗauki alhakin wasu hare-hare a jihohin Kebbi da Sokoto, kuma suna ikirarin alaƙa da ƙungiyar Ansaru wadda ke samun goyon bayan ƙungiyar al-Qaeda.

  20. Burtaniya na binciken zargin samun tsohon sojanta a cikin mayaƙan Ukraine

    Ofishin kula da harkokin ƙasashen waje na Burtaniya da ke Landan ya fara bincike kan rahotannin da dakarun Rasha suka fitar da ke nuna cewa an samu wani tsohon sojin Burtaniya da ke yaƙi tare da dakarun Ukraine.

    An yi amannar cewa ana tsare da matashin a yankin Kursk da ke gabashin Rasha.

    Wakilin BBC ya ce a cikin wani bidiyo da aka yaɗa a intenet, mutumin wanda ke sanye cikin kayan sojoji ya ce sunan shi James Scott Ris Anderson, kuma shekararsa 22.

    Ya ce ya je ne domin taya Ukraine yaƙi saboda ya yi aiki a baya a rundunar sojin Burtaniya.