Gwamnatin Sokoto za ta fara biyan albashi mafi ƙanƙanta na naira 70,000

Asalin hoton, Sokoto State Government
Gwamnatin jihar Sokoto ta amince da fara biyan mafi ƙanƙantar albashi na naira 70,000 ga ma'aikatar jihar.
Cikin wani saƙo da gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya wallafa a shafinsa na Facebook ya ce za a fara biyan sabon albashin ne daga gobe Litinin a faɗin jihar.
Gwamnan ya ce sabon ƙarin albashin ya haɗa da ma'aikatan gwamnatin jiha da na ƙananan hukumomi.
Haka kuma gwamnan ya yi kira ga ma'aikatan jihar su rama wa gwamnati ta hanyar cika mudun aikinsu
Ahmad Aliyu ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da kyautata wa ma'aikatan jihar, ta hanyar biyansu albashi a kan lokaci kowane wata.
Ya kuma alƙawarta ware naira miliyan 500 domin biyan bashin garatutin tsoffin ma'aikata a faɗin jihar.










