Venezuela ta dakatar da yarjejeniyar makamashi da Trinidad & Tobago
Venezuela ta ce ta dakatar da yarjejeniyar makamashin da ta kulla da makwabciyarta Trinidad da Tobago saboda ziyarar da wani jirgin ruwan yakin Amurka ya kai gabar ruwan kasar.
Cikin jawabi daya gabatar ta kafar talbiji ga 'yan kasarsa, Shugaba Nicolas Maduro ya bayyana cewa Caracas za ta dakatar da duk wasu tsare tsare da aka yi akan wani aikin bunkasa makamashi na hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.
Jirgin ruwan na Amurka na aiki ne akan abin da gwamnatin Trump ta ce yaki da kananan jiragen masu ta'ammali da kwayoyi a gabar ruwan kasar.
Mr Maduro ya kira matakin Trinidad na karbar jirgin ruwan yakin Amurka a matsayin cin amana. A ranar Lahadi Mr Maduro ya zargi Amurka da kokarin hambarar da gwamnatinsa.