Majalisar Dinkin Duniya
ta ce ta kaɗu da samun rahotannin da ke cewa an kashe da jikkata da kuma kama
mutane tun bayan zanga-zangar da aka yi a fadin jamhuriyar Kamaru a ranar Lahadi, inda ta
yi kira da a gudanar da bincike tare da kawo ƙarshen tashin hankalin.
Amnesty International
kuwa ta yi kira ne ga gwamnatin Kamarun da ta “girmama, ta kare, ta kuma ba da
damar ‘yancin gudanar da taro cikin lumana.”
Kungiyar ta kuma dage kan
cewa wajibi ne a gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa kan mutanen da
suka mutu, don yin ƙarin haske kan al'amuran da suka faru.
Yayin da take kiran da a
saki duk wadanda aka tsare ba bisa ƙa’ida ba saboda zanga-zangar da ta biyo
bayan zaben, ƙungiyar Human Rights Watch ta buƙaci da a taka wa jami’an tsaron ƙasar birki, ta la’akari da yadda suke amfani da ƙarfin da ya wuce ƙima.
Ilaria Allegrozzi, wata
babbar mai bincike a Human Rights Watch reshen Afirka, ta ce kamata ya yi
jami'an tsaro su kasance suna kare mutane, ba wai suna rura wutar tashin
hankali ba.
A nata ɓangaren ƙungiyar
Tarayyar Turai EU, ita ma ta ce ta damu matuƙa game da yadda aka murƙushe masu
zanga-zangar a ranakun 26 da 27 ga watan Oktoban 2025, tare da nuna rashin jin
dadin yadda wasu fararen hula suka mutu sakamakon harbin bindiga.
Kungiyar ta yi kira ga
mahukuntan Kamaru da su tabbatar da gaskiya da kuma adalci wajen bincikar
zargin amfani da karfin da wuce kima da cin zarafin bil'adama.
Kungiyar Tarayyar Turai ta bukaci dukkan
bangarorin da su kiyaye da kuma kaurace wa duk wani mataki da zai kara
ta'azzara tarzoma