Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/08/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/08/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Usman Minjibir, Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Aljeriya ta yi kira da a ƙaƙaba wa sojojin Mali da sojojin haya na Rasha takunkumi

    Jakadan Aljeriya na Majalisar Dinkin Duniya, Amar Bendjama ya yi kira da a kawo karshen cin zarafi da "dakaru masu zaman kansu" suke yi, a dai dai lokacin da ake samun takun saka tsakanin ƙasar da gwamnatin mulkin sojan Mali da ke samun goyon bayan sojojin haya na kasar Rasha, kamar yadda gidan rediyon Faransa RFI ya ruwaito.

    Sanarwar ta biyo bayan rahotannin hare-haren jiragen sama marasa matuka da aka yi zargin ya ƙashe fararen hula 20 na kasar Mali kusa da kan iyakar Aljeriya a Tinzaouatene.

    Mali ta ce ta kashe wani babban kwamandan mayakan a harin.

    Da yake magana yayin taron Majalisar Dinkin Duniya a ranar 26 ga watan Agusta domin bikin cika shekaru 75 da amincewa da yarjejeniyar Geneva, Bendjama ya yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da ta kakaba takunkumi kan waɗanda ke da alhakin wadannan tashe-tashen hankula.

    Sojojin Mali sun kai hare-hare ta sama a Tinzaouatene a ranar 25 ga watan Agusta a lokacin da suke yaƙi da kawancen 'yan tawaye daga manyan kungiyoyin Abzinawa.

    Har ila yau mayakan da ke kawance da al-Qaeda na ci gaba da kai hare-hare a yankin.

    An mayar da gawarwarkin fararen hulan da aka kashe zuwa Aljeriya domin yi musu jana'iza.

  2. An wanke tsohuwar ministar shari'ar Laberiya daga laifin kisan 'yar uwarta

    Kotun ƙolin kasar Laberiya ta wanke tsohuwar ministar shari'a Gloria Maya Musu-Scott daga zargin kisan ƴar'uwarta da ake yi mata.

    A baya dai wata ƙaramar kotu ta yanke wa Gloria mai shekaru 70, tare da wasu ‘yan uwa mata uku hukuncin ɗaurin rai da rai a kan kisan ƴar'uwar yar shekara 29 mai suna Charlotte Musu a watan Fabrairun 2023, lamarin da ya ɗauki hankulan al’ummar ƙasar.

    Musu-Scott na ɗaya daga cikin fitattun alƙalan ƙasar Laberiya kuma mai fafutukar kare hakkin mata.

    A ranar Larabar da ta gabata ne babban mai shari’a Sie-A-Nyene Yuoh, wanda ke zartar da hukuncin ɗaukaka ƙarar, ya ce shaidun ba su isa su danganta Musu-Scott da ‘yan uwanta da aikata laifin kisar ba, lamarin da ya sa aka wanke su.

  3. Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta'addanci

    Shugaban ƙungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, bisa rakiyar ƴan ƙungiyar ƙwadago da Femi Falana, lauyoyi da suka haɗ da Femi Falana lauya mai rajin kare hakkin ɗanadam a Najeriya da Deji Adeyanju, ya gana da ƴansanda a hedikwatarsu da ke babban birnin tarayya domin amsa gayyatar suka yi masa.

    Rundunar ‘yan sandan dai ta gayyaci shugaban NLC ɗin ne bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta’addanci, wanda shugaban da ƙungiyar suka musanta.

    Tun da karfe takwas na safe ne shugabannin NLC ɗin suka fara hallara a hedikwatarsu, inda suka gudanar da gangamin nuna hadin kai da goyon baya ga Ajaero.

    Bidiyon da aka wallafa a shafin sada zumuntar NLC na X sun nuna wasu shugabannin kwadagon suna jawabi ga ma'aikatan da suka taru, wadanda suka tsaya kyam a bayan Shugaban nasu.

    Kawo yanzu dai babu cikakken bayani na haƙiƙanin abin da ya faru a yayin ganawar.

    Tun da farko dai ‘yan sandan sun gayyaci Ajaero a makon da ya gabata, bisa zargin bayar da kudade ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan sada zumunta.

  4. Yadda sojoji suka harbe wani DPO na ƴansanda a jihar Zamfara

    A wani yanayi mai kama da zaman tankiya tsakanin jami'an soji da na ƴansanda a Najeriya, wani soja ya sa bindiga ya harbe wani DPO na ’yansanda a jihar Zamfara.

    Al'amarin dai ya faru ne a garin Ɗanmarke da ke karƙashin ƙaramar hukumar Bukkuyum ta jihar Zamfara a ranar Larabar nan da daddare, kamar yadda wata sanarwa da rundunar ƴansandan jihar ta Zamfara ta fitar.

    SP Halliru Liman wanda shi ne DPO na Wasugu da ke jihar Kebbi ya gamu da ajalinsa ne a kan hanyarsa ta halartar taronsu na wata-wata, inda sojoji suka tsayar da shi a wani shingen bincike.

    "Duk da cewa ya bayyana musu cewa shi ɗansanda kamar yadda suka buƙata amma kuma sai kawai wani soja mai suna Hassan ya zaro bindiga ya harbe SP Liman a kansa abin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa." In ji sanarwar.

    Rundunar ƴansandan ta jihar Zamfara ta nemi da dukkan hukumomin da suke da ruwa da tsaki da su gudanar da cikakken bincike na yadda al'amarin ya faru.

    "Abin da sojojin suka yi ya fito fili da irin rashin son aiki tare da sauran jami'an tsaro," kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

  5. Wataƙila Madrid ta haɗu da Man City da Bayern da PSG a sabon tsarin Zakarun Turai

    Da maraicen yau Alhamis ne za a raba jadawalin sabon tsarin Zakarun Turai na Champions League da za a fara amfani da shi a kakar wasa ta bana.

    Muhimmin sauyi da kwamitin zartarwa na UEFA ya sanar shi ne ficewa daga tsarin matakin rukuni da ake yi a baya.

    A baya matakin rukuni na gasar Zakarun Turai ya ƙunshi ƙungiyoyi 32, da ake raba wa cikin rukuni takwas, inda kowanne rukuni ke ƙunshe da ƙungiyoyi huɗu.

    A sabon tsarin na yanzu kowace ƙungiya za ta kara da ƙungiyoyi takwas( huɗu a gida hudu a waje), ba aihinin tsarin rukuni da aka saba yi ba.

    Shin yaya raba jadawalin sabon tsarin zai kasance? Ku shiga nan

  6. Yadda gobarar dajin Canada ta gurɓata iska a duniya - Bincike

    Wani sabon bincike ya gano cewa mummunar gobarar dajin da ta auku a Canada a bara, ta fitar da gurɓatacciyar iska fiye da adadin da ake ƙonewa a ƙasashen duniya idan aka cire ƙasashe uku.

    Amurka da China da India ne kawai suka fi fitar da gurbatacciyar iska a 2023.

    Gobarar dajin ta laƙume yankuna da dama na dazukan Canada tare da raba kimanin mutum 200,000 da gidajensu.

    Masu bincike sun yi nazari ne kan hotunan tauraron dan'adam na hayaƙin da ya turnike samaniya wajen ƙididdige yawan adadin gurbatacciyar iskar.

    Sun yi gargɗin cewa yanayin zafi da ya haifar da gobarar zai iya zama wani abin da za a ci gaba da gani har nan da shekarar 2050.

  7. Najeriya ta fara shirin kwashe mutane daga wuraren ambaliya

    Darakta-Janar ta Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa, NEMA, Zubaida Umar, ta ce hukumar ta fara shirin aikin kwashe jama'ar da ke fuskantar barazanar ambaliyar ruwan sama zuwa kan tuddai.

    A daidai lokacin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar mamakon ruwan sama, NEMA ta ce ambaliyar ruwa ta shafi jihohi 28, inda mutum 175 suka mutu, sannan mutum 207,902 suka rasa muhallansu.

    Hukumar ta ce ambaliyar ta shafi mutum 526,703 a ƙananan hukumomi 133, inda lamarin ya shafi gidaje 79,138 da kuma hekta 106,178 na gonaki.

    Domin fuskantar wannan yanayin ne, gwamnonin jihohi da NEMA ta fara kwashe mutane daga wuraren da suke fuskantar barazanar ambaliyar domin rage ɓarnar.

    Ta ƙara da cewa NEMA za ta buɗe cibiyoyinta domin sauƙaƙa ayyukan hukumar domin jiran kar ta kwana.

    Wannan na zuwa ne bayan ziyarar Shugaban Ma'aikatan Gidan Gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila a hukumar, inda ya je domin duba yadda ake gudanar da ayyukan hukumar bayan wani taron ƙara wa juna sani da ya yi da hukumomin da ke ƙarƙashin Fadar Shugaban Ƙasa.

    Darakta-Janar ɗin ta kuma buƙaci ƙarin haɗin kai daga kwamitin majalisa da sauran masu ruwa da tsaki domin faɗaɗa ayyukan NEMA da shirye-shiryenta na fuskantar ayyukan agajin gaggawa.

  8. Ƴansanda sun yi arangama da ƴan fansho masu zanga-zanga a Argentina

    'Yan sanda sun yi arangama da ƴan fansho masu zanga-zanga a Buenos Aires babban birnin Argentina.

    Masu zanga-zangar dai sun taru ne domin nuna adawa da sanarwar shugaban kasar ta yin watsi da karin albashin da aka riga aka amince.

    ‘Yan sandan kwantar da tarzoma sun harba hayaƙi mai sa hawaye tare da dukan wasu daga cikin yan fansho ɗin a lokacin da suke gudanar da zanga-zangar kusa da ginin majalisa.

    'Yan adawar ƙasar sun yi Allah wadai da baza jami'an tsaro kan masu zanga-zangar.

    A makon da ya gabata ne majalisar dattawan Argentina ta amince da ƙudirin yin ƙarin albashi ga yan fansho la'akari da halin hauhawar farashin kayayyaki da ƙasar ke fama da shi.

    Amma shugaban ƙasar Javier Milei ya ce ba zai amince da matakin ba, wanda ya ce cikas ne ga matakan gwamnatinsa na ƙara tsuke bakin aljihu.

  9. Sojojin Nijar da suka mutu a harin ƴan bindiga sun kai 24

    Sojojin da suka mutu a harin da ake zargin ƴan bindiga ne suka kai a kan jami'an tsaro a yankin Yammacin Tillaberi na Jamhuriyar Nijar a ranar 27 ga Agusta sun haura zuwa 24, kamar yadda kafar rahotanni daga kafar watsa labaran tsaro ta African Maps security blog ya nuna.

    Da farko kafar ta ruwaito cewa aƙalla sojoji bakwai ne suka mutu a harin, wanda aka kai a sansanin sojoji da ke Bouloundjounga.

    Amma daga baya da sojojin ƙasar suka kai ɗauki, sun sake gano wasu gawarwakin guda 17, inda jimilla ta zama 24.

    Bayan haka kuma akwai gomman sojoji da har yanzu babu labarinsu, kamar yadda rahoton ya nuna a shafin X.

    Talabijin na RTN Tele Sahel ya ruwaito cewa sojojin ƙasar sun kashe sama da ƴan bindiga guda 50, amma ba a ruwaito labarin kashe sojojin ba.

    Wannan harin na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban sojin ƙasar, waɗanda suka karɓe mulki bayan hamɓarar da Mohamed Bazoum ke cigaba da yaƙi da ƙungiyoyi ƴan bindiga masu iƙirarin jihadi, musamman masu alaƙa da al-Qaeda.

  10. MDD ta nemi Isra'ila ta fice daga Yamma da Kogin Jordan

    Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira ga Isra'ila ta gaggauta dakatar da ayyukan sojinta a Gaɓar yamma da kogin Jordan da ta mamaye.

    Sanarwar da Mista Guterres ya fitar ta ce yanayin na ƙara muni sosai. Jami’an Falasdinawa sun ce aƙalla mutum 11 aka kashe a wani farmakin da Isra'ila ta kira na yaki da ta'addanci.

    Farmakin sojojin dai ya janyo hasarar rayuka da lalata gidaje da abubuwan more rayuwa a Jenin da Tulkarm da Nablus da kuma Tubas.

    Wannan dai shi ne farmaki mafi girma na Isra'ila a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan fiye da shekaru ashirin.

    Shugaban Falasɗinawa Mahmud Abbas ya soke ziyarar da yake yi a ƙasar Saudiyya.

  11. Yau ake fara gasar Paralympics a birnin Paris

    A yau ne ake fara wasannin nakasassu wato Paralympics a birnin Paris - inda za a lashe lambobin yabo a tseren keke da ninƙaya da table tennis.

    A gagarumin bikin buɗɗe wasannin da aka yi a daren Laraba, shugaban kwamitin shirya wasannin ya ce yana son wasannin na bana su kayatar waɗanda suka ƙunshi har da sabbin ƴanwasan da ba a taba gani ba.

    Dimbin jama'a ne suka taru domin ganin yanwasa da dama daga sassan duniya.

  12. An bayar da belin mai shafin Telegram a Faransa

    An bayar da belin hamshakin attajirin ɗan asalin ƙasar Rasha kan Dala miliyan biyar da rabi, tare da hana shi barin Faransa.

    Mista Durov na fuskantar tuhume-tuhume da dama da suka haɗa da gazawa wajen daƙile ayyukan ƴan ta'adda da abubuwan da ba su dace ba a dandalin musamman yaɗa hotunan cin zarafin yara.

    Kusan mutum biliyan ɗaya ne ke amfani da dandalinsa na Telegram.

    An dai tsare Mista Durov ne tsawon kwana huɗu a Faransa a wani ɓangare na bincikensa kan aikata manyan laifuka.

    Tuni dai lauyansa ya yi watsi da zarge-zargen da ake masa inda ya ce dandalin na Telegram ya kiyaye dokoki da sharuɗɗan amfani da intanet na Turai.

  13. Zargin taimakon ta'addanci: Yau shugaban NLC zai bayyana a gaban ƴansanda

    A yau ne Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago, Joe Ajaero zai amsa gayyatar ƴan sanda domin amsa wasu tambayoyi game da zarginsa da ɗaukar nauyin ta'addanci da laifukan kafofin sadarwa da cin amanar ƙasa da sauransu.

    A ranar Talatar ta da gabata ne wato 20 ga watan Agusta ƴan sandan suka gayyaci shi ya bayyana a gabansu bayan wani samame da suka kai a sakatariyar NLC da ke Abuja.

    Amma shugaban NLC ɗin ya bayyana cewa zai mutunta gayyatar a ranar Alhamis, 29 ga watan Agustan, maimakon ranar da ƴansandan suka buƙata da farko.

    "Ƴan sandan sun ce sun yi samamen ne domin gano wasu muhimman abubuwa da suke da alaƙa da zanga-zangar matsin rayuwa da aka yi a Najeriya,"

    Domin nuna goyon baya ga Ajaero, Ƙungiyar Ƙwadago ta umarci mambobinta a faɗin ƙasar da su taru a hedkwatar ƴan sanda na jihohinsu, "har sai shugabansu ya bar hedkwatar ƴan sandan."

    Ƙungiyar Ƙwadagon dai a makon da ya gabata ta yi gargaɗi tare da yin barazanar fara yajin aikin sai baba-ta-gani, idan har aka kama shugabanta, Joe Ajaero.

    Idan ba a manta ba, dubban mutane ne suka fito suka yi zanga-zangar matsin rayuwa, ƙarƙashin jagorancin wata ƙungiya mai suna Coalition of Concerned Nigerian Citizens.

  14. Assalamu Alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga nan sashin Hausa na BBC, inda za mu riƙa kawo muku labaran muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Ku kasance tare da mu a wannan shafin.

    Sannan za ku iya leƙawa shafinmu na kafofin sadarwa domin kallon bidiyoyi da hotuna.