'Harin Amurka ya saɓa wa dokar ƙasa da ƙasa'

Jakadan Iran a Birtaniya, Seyed Ali Mousavi, ya bayyana cewa harin da Amurka ta kai Iran ya "saɓa wa dokar ƙasa da ƙasa".
Ya bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da BBC, sai dai ya ki cewa uffan lokacin da aka tambaye shi kan irin ɓarnar da harin ya yi kan cibiyoyin nukiiyar Iran.
Ya ce hare-haren sun kuma saɓa wa ƴancin ƙasar Iran.
Wakiliyar BBC Laura Kuenssberg ta tambaye shi ko Iran za ta yi watsi da shirinta na nukiiya da kawo karshen rikicinta da Isra'ila idan Amurka ta sake far mata.
Mousavi ya ce Iran da Amurka na cikin tattaunawa kan shirin nukiliya kafin "Isra'ila ta far mana".






