Me zai bambanta zaɓen Najeriya mai zuwa da waɗanda suka gabata?

Ƴan Najeriya na sa ran ganin sauye-sauye a hanyoyin gudanar da zaɓukan ƙasar a zaɓen 2027 da ke tafe nan da shekara guda.
Ana sa ran ganin sauye-sauyen ne bayan fara aiki da sabuwar dokar zaɓen ƙasar da aka yi wa gyaran fuska.
A makon da ya gabata ne shugaban ƙasar da ya sanya hannun kan sabuwar dokar zaɓen ƙasar ta 2026, in da aka samar da manyan gyare-gyare, wadanda za su shafi tsarin gudanar da zaɓukan ƙasar.
Sauye-sauyen na zuwa ne bayan ƙorafe-ƙorafen ƴan ƙasar, kan wasu dokokin zaɓen ƙasar da suke ganin ba su dace da yanayin ƙasar ba.
An dai kai ruwa rana a majalisar dokokin ƙasar kafin amincewa da sabbin dokokin, lamarin da ya kai ƙungiyoyin fararen hula shirya zanga-zangar matsin lamba ga majalisar dokokin ƙasar domin amincewa da sakamakon.
An ɓullo da sauye-sauyen masu yawa a tsarin zaɓen ƙasar, kama daga kan fitar da ƴan takara zuwa yakin neman zaɓe da ma tattara sakamako.
Masu sharhi kan al'amuran siyasa na ganin akwai sauye-sauye da za a gani a tsarin zabukan kasar masu zuwa.
