Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 18/06/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. Yaƙin Iran da Isra'ila zai iya sa a manta da wahalar da muke ciki - Falasɗinawa

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    A Gaza, falaɗinawa na bayyana ra’ayoyinsu dangane da sabon rikici tsakanin Iran da Isra’ila.

    Wasu sun nuna jin daɗin ganin hare-haren Iran sun shafi Isra’ila, amma da dama sun ce hakan yana ƙara kau da hankalin duniya daga wahalhalun da suke ciki tsawon watanni 20.

    Hassan Omar Talba, wanda ya rasa iyalinsa a harin Isra’ila, ya bayyana taƙaici dangane da irin tallafin da Iran ke iƙirarin bayarwa a Gaza.

    “Iran ba ta taɓa gina makaranta ko asibiti ko aika da motar bayar da agaji zuwa Gaza ba,” in ji shi.

    “Abin da suka yi kawai shi ne aika roka da marawa Hamas baya, wanda hakan ya kara dagula rayuwarmu.”

    Duk da haka, ya kara da cewa, “Ina goyon bayan duk wanda ke kai hari kan Isra’ila. Aƙalla fararen hular Isra’ila su ɗanɗana irin wahalar da muke ciki a Gaza, ko da na dare ɗaya ne.”

    Alaa Saleh, uba ga yara biyar, ya bayyana damuwa iri daya da Omar.

    “Yaƙin da ke faruwa a Gaza har yanzu bai tsaya ba. Mutuwa da yunwa da gudun hijira sun zama ruwan dare a rayuwarmu. Amma yanzu duniya na mai da hankali kan abin da ke faruwa a Iran. Ko kafafen yada labarai sun daina bayar da rahotanni daga Gaza.”

  2. Sojojin Isra'ila sun sake kai hari a wuraren nukiliyar Iran

    Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi tsakanin Isra'ila da Iran, mazauna birnin Tehran sun ba da rahotannin jin ƙarar fashe-fashe a babban birnin da kuma birnin Karaj mai maƙwabtaka.

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce sojojin Isra'ila ne suka kai hari kan cibiyoyin ƙera makami mai linzami da nukliyar Iran.

    Rundunar sojin Isra'ila tun farko ta shawarci mutane a wata gunduma da ke Tehran da su fice daga gidajensu inda suka ce suna shirin kai hari.

    Iran ta ce ta harba makamai masu linzami kan Isra'ila. Kawo yanzu babu rahoton rasa rai.

  3. Amurka na tunanin tallafa wa Isra'ila wurin kai hare-hare a Iran

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da hari kan cibiyoyin ƙera makami mai linzami da na nukiliya a Iran yayin da Shugaba Donald Trump ke tattauna yiwuwar sojojin Amurka su shiga yaƙin.

    Hakan na nufi da cewa akwai zaɓi uku ga Shugaba Trump ko dai ya shiga yaƙin, ko ya tsame kansa ko kuma ya nemi a tattauna.

    Rundunar IDF ta ce an aika jiragen yaƙin Isra'ila sama da hamsin a rana ta shida na yaƙin.

    Sai dai Amurka ce kaɗai take da ikon kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran na ƙarƙashin ƙasa hari.

    Rahotanni na cewa an samu rarrabuwar kai a majalisar tsaron Amurka kan matakin da ya fi dacewa ƙasar ta ɗauka amma Trump ya yi wata tattaunawa ta waya da Firaiministan Isra'ila.

  4. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a hantsin Laraba.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassa na duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.