Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 24/11/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 24/11/2025

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Isiyaku Muhammed da Aisha Aliyu Jafar

  1. Ƴansandan Ghana sun kama wanda ake zargi da kashe jami'ar kiyaye haɗuran Najeriya

    Ƴansanda

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴansanda a Ghana sun ce sun samu nasarar kama wani ɗan Najeriya mai suna Victor Benjamin Fajemirokun wanda ake zargi da kashe wata jami'ar hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya da ƴarta a jihar Ogun da ke kudu maso yammacin ƙasar.

    Kwamandan sashen Gabas maso Kudanci a rundunar ƴansandan ƙasar Ghana, George Ohene-Boadi ne ya bayyana haka a taron ganawa manema labarai, inda ya ce wanda ake zargin mai shekara 36 ya tsere zuwa Ghana ne bayan ya yi aika-aikar.

    Ya ce sun ga wani bidiyo ne wanda a ciki ake zargin matashin da sacewa tare da kashe jami'ar mai suna Lasisi Funmilayo da ƴarta Sewa a garin Abeokuta da ke jihar Ogun, sannan ya tsere.

    "Ƴansandan Najeriya ne suka fara nemansa ruwa a jallo, maimakon ya miƙa kansa sai ya tsere zuwa Ghana," in ji Ohene-Boadi.

    Ɗansandan ya ce yanzu haka wanda ake zargin yana hannunsu, "sannan idan muka kammala bincikenmu a nan za mu miƙa shi ga hukumomin Najeriya."

  2. 'Daftarin tsagaita a Sudan da Amurka ta tsara ya munana'

    RSF

    Asalin hoton, AFP

    Shugaban rundunar sojin Sudan ya bayyana daftarin daftarin da Amurka da kuma masu shiga tsakani wajen kawo karshen yakin da ake kasar suka mika musu a matsayin mafi muni wanda ba a taba gabatar da wani makamancinsa ba a baya.

    Cikin wani bidiyo, Janal Abdel Fattah al Burhan, ya ce shirin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninsu da mayakan RSF zai kawar da ayyukan sojoji sannan kuma zai bai wa mayakan dama su ci gaba da kasancewa a yankunansu.

    Shugaban rundunar sojin ya zargi Jakadan Amurka Massad Boulos da yin magana da a madadin Hadaddiyar Daular Larabawa, wadda tana daya daga cikin masu shiga tsakanin da ake zargi da goyon bayan mayakan na RSF.

  3. UNICEF ta cimma yarjejeniyar rage farashin allurar rigakafin malaria

    sauro

    Asalin hoton, Other

    Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya cimma yarjejeniya domin rage farashin allurar rigakafin cutar zazzabin cizon sauro wato malaria wadda zata ya kare yara maza da mata miliyan bakwai da ga cutar zuwa nan da shekarar 2030.

    Farashin allurar rigakafin samfurin R21, wanda yanzu yake kan kudi dala hudu zai koma dala uku sakamakon yarjejeniyar da aka cimma da kamfanin daya samar da ita wato GAVI.

    Kudin da aka ragen zai ba wa kasashe damar siyan adadi mai yawa.

    Har yanzu cutar malaria na daya daga cikin cutukan da suke da mummunar illa a duniya inda Majalisar Dinkin Duniya ta ce yaro daya na mutuwa a kowanne minti daya sakamakon cutar.

  4. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin, daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu ɗaura daga inda muka tsaya a jiya a wannan shafin na labaran kai-tsaye.

    Ku kasance tare da mu.