Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 06/07/2024

Labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 06/07/2024

Taƙaitattu

  • Shugabannin ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso na taro a Yamai
  • Harin Rasha ya katse hanyoyin ruwa a yankin Sumy na Ukraine
  • Mai ra'ayin kawo sauyi ya lashe zaɓen Iran
  • Shin Ronaldo ya buga wa Portugal wasan ƙarshe?
  • Starmer zai jagorancin taron majalisar zartarwa na farko bayan kafa gwamnati

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza da Badamasi Abdulkadir Mukhtar

  1. Shin Ronaldo ya buga wa Portugal wasan ƙarshe?

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Cristiano Ronaldo ya fice daga filin wasa cike da takaicin rashin nasara da Portugal ta yi a hannun Faransa a bugun fenareti bayan da ƙasashen biyu suka tashi babu ci a gasar Euro 2024 da ake bugawa a Jamus.

    Masu bibiyar ƙwallon ƙafa da dama na ganin wataƙila wasan ya zama na ƙarshe da Ronaldo, mai shekara 39 ya buga wa ƙasar tasa.

    To sai dai kocin Portugal Roberto Martinez ya ce ''har yanzu Ronaldo bai yanke hukunci ko zai ci gaba da taka wa ƙasar leda ko akasin haka ba.

    Tsohon tauraron na Real Madrid da Manchester United ya buga duka wasanni biyar da Portugal ta yi a gasar ta bana.

    A wasan zagayen 'yan 16 ne Ronaldo ya sharɓi kuka bayan da ya kasa cin bugun fenareti da ƙasarsa ta samu a ƙarin lokaci a wasansu da Sloveniya, kodayake daga baya Portugal ta yi nasara a bugun fenareti.

    Wannan ne ya sa magoya bayan ƙwallon ƙafa ke yi masa kallon mutum mai kishin ƙasarsa a fannin tamaula.

    Baya ga Ronaldo akwai Pepe - wanda ya kafa tarihin zama mutum mafi yawan shekaru, 41 - da ya buga gasar Euro.

    'Yan wasan biyu - waɗanda suka taka leda tare a Real Madrid - sun rungume juna bayan tashi daga wasan, yayin da Pepe ke sharɓar kuka Ronaldo na rarrashinsa.

  2. Harin Rasha ya katse hanyoyin ruwa a yankin Sumy na Ukraine

    .

    Asalin hoton, .

    Jami'an ƙasar Ukraine sun ce wani harin da jiragen saman Rasha suka kai ya katse hanyoyin samar da ruwan sha a yankin Sumy da ke arewa maso gabashin ƙasar.

    Harin da aka kai a safiyar ranar Asabar ya kakkaɓo wayoyin lantarkin da ke tura ruwan sha ga jama'a.

    An daɗe ana samun katsewar lantarki a yawancin Ukraine sakamakon hare haren da Rasha ke kaiwa kan kayayyakin more rayuwa na ƙasar.

  3. Shugabannin ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso na taro a Yamai

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Nan gaba a yau ne shugabannin mlkin sojin ƙasashen Mali da Burkina Faso da Nijar za su gudanar da taronsu domin kammala ficewarsu daga ƙungiyar Ecowas, tare da sanar da kafa sabuwar ƙungiyar ƙawancen yankin Sahel.

    Za a gudanar da taron ne a Yamai, babban birnin Jamhuriyar Nijar Nijar domin ƙaddamar da sabuwar ƙungiyar tasu a hukumance.

    Taron ƙasashen uku na zuwa ne a jajibiren taron ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka ta ECOWAS, ko CEDEAO.

    A watan Janairu ne ƙasashen uku suka sanar da ficewa daga Ecowas don nuna adawa da takunkumin da ƙungiyar ta ƙaƙaba musu.

    Gwamnatocin sojan ƙasashen sun yanke hulda da Faransa, tsohuwar uwar gijiyarsu, inda yanzu suke ɗasawa da Rasha, da Turkiyya da kuma Iran.

  4. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkan mu da safiya.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a faɗin duniya.

    Sai ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tamfa muhawa kan labaran da muke wallafawa.