Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na yau Talata 4 ga watan Fabrairun 2025

Taƙaitattu

  • Najeriya ta ware fiye da naira biliyan 4 don yaƙi da HIV
  • Mutum huɗu sun mutu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Neja
  • An kashe sojojin Isra'ila biyu a Gaɓar Yamma
  • Majalisar Dokokin Najeriya za ta koma zama a yau
  • An yanke wa mutum biyar hukuncin kisa a Kano bayan kashe tsohuwa bisa zargin maita
  • Kasuwannin hannayen jari na Asiya sun sake farfaɗowa
  • Ƴantawayen M23 sun tsagaita wuta a Congo

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi, Aisha Aliyu Ja'afar, Umaymah Abdulmumin da Ahmad Bawage

  1. An kafa kwamitin da zai laluɓo hanyar gudanar da zaɓe a Libya

    Shirin tallafawa ƙasar Libya na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce ya kafa kwamitin da zai nemi hanyoyin warware takaddamar da ke kawo tsaiko wajen gudanar da zaɓukan da aka daɗe ana jira.

    A shekarar 2021 ne ya kamata a ce an gudanar da zaɓukan ƙasar, sai dai an yi watsi da shirin saboda takaddamar da aka riƙa yi a kan cancantar ƴan takara.

    Ana dai fatan zaɓen zai taimaka wajen kawo karshen rikicin da aka shafe fiye da shekaru 10 ana yi a ƙasar, wanda gwamnatoci da ke gaba da juna a gabashi da yammaci ke ruruta wa.

    A makon gobe ne kwamitin zai yi ganawarsa ta farko a birnin Tripoli.

  2. Za a fara cin tarar masu yin ƙazanta a titunan Kano naira 25,000

    Ƙudirin haramci da saka tarar naira 25,000 ga duk mutumin da aka kama yana ba-haya ko fitsari ko zubar da shara da tofa yawu da majina a tituna da ƙarƙashin gadoji da gine-ginen gwamnati da ma wuraren taruwar al'umma al'umma, da majalisar dokokin jihar Kano ta amince da shi, na ci gaba da tayar da ƙura a jihar.

    A ranar Litinin ne dai majalisar dokokin jihar ta amince da ƙudirin inda kuma za ta miƙawa gwamnan jihar domin sanya masa hannu wanda daga nan ne kuma zai zama zama doka.

    Idan har gwamna ya amince da ƙudirin, duk wanda aka samu da laifi kuma ya gaza biyan tarar ta naira 25,000 to hakan ka iya kaiwa ga kotu ta tasa ƙeyar mutum zuwa gidan yari.

  3. Majalisar zartarwa ta amince da aiwatar da ayyuka 100 a faɗin Najeriya

    Majalisar zartarwa ta Najeriya ta amince da aiwatar da wasu ayyuka da shirye-shirye kimamin 100 da za a yi a fadin kasar.

    Majalisar ta amince da haka ne a yau Talata a zamanta na farko a wannan shekara ta 2025.

    Yawancin ayyukkan da aka amince da su yayin zaman wanda aka fara jiya Litinin, sun jiɓanci fannin hanyoyi da kiwon lafiya da kuma shirye-shiryen haɓaka tattalin arziki.

  4. Mutum huɗu sun mutu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Neja

    Wani hatsarin mota a karamar hukumar Agaie na jihar Neja ya janyo mutuwar wasu mutum huɗu.

    Lamarin wanda ya afku kan hanyar Agaie zuwa Lapai, ya jikkata mutane 13.

    Wata sanarwa da darekta-janar na hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar (NSEMA) Abdullahi Baba-Arah ya fitar, ya ce hatsarin ya afku ne sakamakon garuwa da wasu tireloli uku suka yi da juna, inda ɗaya daga cikinsu ke ɗauke dabbobi.

    "Hatsarin ya yi muni, nan take mutum biyu suka mutu yayin da sauran biyu kuma suka cika a asibiti," in ji Abdullahi.

    Jami'in hukumar ta ba da agajin gaggawa a jihar ya ce tuni aka garzaya da waɗana suka jikata zuwa babban asibitin Agaie kuma suna cigaba da karɓar magani.

    Ya ce ba ya ga asarar rayuka - lamarin ya kuma rutsa da shanu 15 da akuyoyi sama da 20.

  5. Jiragen sama ɗauke da ƴan ci-rani daga Amurka sun doshi Guantanamo Bay

    Amurka ta ce jiragen farko da ke ɗauke da yan ci-rani sun doshi sansanin sojojinta da ke Guantanamo Bay a ƙasar Cuba.

    Mai magana da yawun fadar White House, Karoline Leavit, ta ce jiragen saman sojojin ƙasar na ɗauke ne da mutanen da suka shigo ƙasar ta haramtacciyar hanya.

    A cewarta Amurka ta daina zama wurin zuwan masu aikata miyagun laifuka daga wasu ƙasashen waje.

    An dai yi amfani da sansanin na Guantanoma Bay wajen tsare mutane da ake zarginsu da ta'adanci bayan hare-haren ranar 9 ga watan Satumbar shekarar 2001.

  6. Ƴan sanda sun ce an kashe mutum aƙalla 10 a wata makaranta a Sweden

    Ƴan sanda sun ce aƙalla mutum 10 ne aka kashe a harbi a wata makaranta a Sweden, ciki har da ɗan bindigar da ya kai harin.

    Harbin da aka yi a makarantar Risbergska a birnin Orebro, mai nisan kilomita 200 daga babban birnin ƙasar Stockholm, ya faru ne da ranar Talata.

    Ƴan sanda sun ce ba su mutumin da ake zargi da kai harin ba da kuma dalilinsa na yin haka.

    Sun yi gargaɗi a yammacin yau Talata cewa alkaluman waɗanda suka mutu zai ci gaba da ƙaruwa, yayin da mutane da dama suka jikkata.

    "Wannan lamari ne mai muni," in ji shugaban ƴan sanda na birnin Orebro Roberto Eid Forest.

    Tun da farko, Firaministan Sweden ya ce "rana ce mai bakin ciki ga dukkan ƴan Sweden".

    An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti, inda ake yi wa aƙalla huɗu aiki.

  7. Ƴan sanda sun kuɓutar da mutum uku da aka sace, sun ƙwace makamai a Edo

    Rundunar ƴan sanda a jhar Edo ta ce ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su.

    Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Moses Yamu ya fitar, ya ce an yi garkuwa da mutanen ne a watan da ya gabata lokacin da suke kan hanyar zuwa Onitsha daga Abuja.

    "Ƴan sanda tare da haɗin gwiwar wasu jami'ai ne suka bi tsawun masu garkuwan, inda kuma suka yi nasarar kuɓutar da mutanen da suka tafi da su," in ji sanarwar.

    A gefe guda, rundunar ta ce ta ƙwato bindigar AK-47 da kuma harsasai yayin samame da ta kai.

  8. Mbappe da Bellingham za su yi jinya

    Real Madrid za ta buga Copa del Rey ba tare da Kylian Mbappe da Jude Bellingham ba, in ji koci Carlo Ancelotti.

    Ranar Laraba Laganes za ta karɓi bakuncin Real Madrid a Copa del Rey zagayen kwata fainals.

    Mbappe da Bellingham za su bi sawun masu jinya a ƙungiyar da suka haɗa da Eduardo Camavinga da David Alaba da Antonio Rudiger da kuma Eder Militao da Dani Carvajal da suka daɗe suna jinya.

    Mbappe ƙyaftin ɗin tawagar Faransa, mai shekara 26 ya ci ƙwallo 21 a wasa 33 tun bayan da ya koma Santiago Bernabeu a kakar nan daga PSG.

    Shi kuwa Bellingham ɗan ƙwallon tawagar Ingila, mai shekara 21 ya zura ƙwallo 10 a wasa 30 a ƙungiyar ta Sifaniya.

    Madrid, wadda take ta ɗaya a kan teburin La Liga da maki 49 bayan wasa 22 tana da tazarar maki ɗaya tsakaninta da Atletico Madrid ta biyu, Barcelona ce ta uku.

  9. Najeriya ta ware fiye da naira biliyan 4 don yaƙi da HIV

    Gwamnatin Najeriya ta amince da kashe naira biliyan 4.8 wajen yaƙi da yaɗuwar cutar HIV a ƙasar.

    Wannan na daga cikin matsayar da aka cimma a taron majalisar zartarwa ta tarayya, inda gwamnatin ta sanar da ware fiye da dala biliyan ɗaya ga ɓangaren lafiyar ƙasar.

    Gwamnatin ta ce wannan yana daga cikin manufofinta na inganta kiwon lafiya a matakin farko.

    Ta ce ta tsara kashe kuɗaɗen ne a fannin ɗaukar ma’aikatan lafiya da bayar da horo gare su domin samun ƙwarewa da kuma tabbatar da an bayar da kulawar da ta kamata don hana yaɗuwar cutar HIV a sassan ƙasar.

    A baya dai an riƙa bayyana damuwa game da sabbin tsare-tsaren da gwamnatin shugaban Amurka, Donald Trump ta ɓullo da su, musamman a fannin bayar da tallafi, inda ake tunanin za su iya shafar tallafi ga yaƙi da cutar HIV a ƙasashe masu tasowa.

    Amma a ranar Asabar gwamnatin Amurkan ta sanar da ware sabon ƙunshin tallafin yaƙi da cutar ta HIV.

    Alƙalumman da hukumar hana yaɗuwar cutar HIV a Najeriya ta fitar, sun ce ƙasar ce ta fi kowacce yawan masu cutar a yammacin Afirka, kuma an daɗe ana samun kiraye-kiraye daga faɗin duniya na ganin Najeriya ta zage damtse wajen yaƙi da yaɗuwar cutar.

  10. Dubban mutane na tserewa daga tsibirin Santorini saboda fargabar girgizar ƙasa

    Dubban mutane sun bar gidajensu da ke tsibirin Santorini da ke Girka saboda tsoron girgizar ƙasa.

    A cewar kafafen yaɗa labaran tsibirin, mutane 6,000 ne suka bar yankin ta ruwa tun daga ranar lahadi, yayin da jiragen saman gaggawa ke shirin tashi a yau Talata.

    An samu fiye da girgizar ƙasa 300 a cikin kwanaki biyu da suka gabata kusa da tsibirin, kuma wasu ƙwararrun na cewa za a cigaba da samun motsin ƙasa a makonnin masu zuwa.

    Hukumomi sun kulle makarantu na tsawon makon, kuma sunyi gargaɗi kan taruwar mutane dayawa a cikin gida, sai dai Firaminista Kyriakos Mitsotakis ya buƙaci a kwantar da hankali.

    Santorini wani sannanen wuri ne na yawon buɗe ido wanda ya shahara saboda fararen gine ginensu, sai dai mutanen da ke tafiya akasari yan tsibirin ne ganin cewa Fabrairu ba lokacin da aka fiye zuwa yawon buɗe idon bane.

    An samu motsin ƙasa da dama da ya kai ƙarfin 4.7 a arewa maso gabashin Santorini a safiyar yau Talata.

    Duk da dai zuwa yanzu ba a samu ɓarna mai girma ba, ana cigaba da ɗaukar matakan kariya.

  11. MDD ta buƙaci a sake buɗe filin jirgin sama na Goma

    Majalisar ɗinkin duniya ta yi kira a sake buɗe filin jirgin sama na garin Goma da ke gabashin Jamhuriyar Dimokraddiyar Kongo ba tare da ɓata lokaci ba, domin taimakawa wajan shawo kan matsalar jin ƙai.

    A makon da ya gabata ne garin ya faɗa hannun mayaƙan ƴan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda kuma ɗaruruwan mutane aka kashe a faɗan da aka yi tsakanin dakarun ƙasar da mayaka masu tayar da ƙayar baya.

    Jami'in kula da ayyukan jin ƙai na MDD ya bayyana filin jirgin saman a matsayin muhimiyar hanyar ceto rayukan mutane.

    Bruno Lemarquis ya ce akwai mutane da dama da aka raunata waɗanda ke matuƙar buƙatar kulawar asibiti da magani kuma marasa lafiya sun yi yawa a asibitocin da suka rage.

    Mayaƙan M23 sun ayyana tsagaita wuta wadda ya kamata a ce ta fara aiki.

  12. Netanyahu zai gana da Donald Trump

    Firaminstan Isra'ila Benjamin Netanyahu zai gana da Shugaban Amurka Donald Trump a Washington a yau domin tattaunawa.

    Ana sa ran tattaunawar za ta mayar da hankali kan tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.

    Mista Trump ya bayyana cewa ya na so yaƙin ya zo karshe, sai dai Netanyahu na fuskantar matsi daga ɓangaren masu tsattsauran ra'ayi kan cigaba da yaƙin har sai an ci galaba kan Hamas.

    Gabanin taron, an harbe sojojin Isra'ila biyu kusa da birnin Tabas a gaɓar Yamma.

    Lamarin na zuwa ne a yayin da sojojin Isra'ila ke cigaba da kai munanan hare-hare kusa da birnin Jenin.

  13. An kashe aƙalla fararen hula 90 a Sudan

    An kashe gomman fararen hula a Sudan yayin da ake cigaba da gwabza yaƙi tsakanin sojoji da dakarun RSF.

    Rahotanni sun bayyana cewa harin saman da ake zargin sojoji sun kai ranar Litinin a wuraren da ke ƙarƙashin ikon RSF a birnin Nyara da ke kudancin Darfur, ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla fararen hula 30.

    A gefe guda kuma ana ganin fiye da fararen hula 60 ne suka mutu bayan dakarun RSF sun harba manyan makamai a birnin el Fasher.

    Har yanzu dai ba a tabbatar da waɗanda ke da alhakin kai harin ba ko kuma girman ɓarnar da ya yi saboda hana shiga yankin da aka yi.

    Ana cigaba da samun ƙaruwar kai hare-hare a cikin kwanakin nan a yankin.

    A ƙarshen makon da ya gabata ma an kai hari wata kasuwa a birnin Omdurman da yayi sandiyyar mutuwar gomman mutane wanda kuma ake zargin rundunar RSF ne suka kai harin.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana harin Omdurman a matsayin ''keta dokokin kare haƙƙin bil Adama''.

  14. An kashe sojojin Isra'ila biyu a Gaɓar Yamma

    Rundunar sojin isra'ila ta ce an hallaka sojojinta biyu tare da jikkata wasu shida a harin da aka kai kan wani wurin binciken sojoji kusa da birnin Jenin a Gaɓar Yamma.

    Sai dai an samu nasarar kashe maharin a yayin da aka yi musayar wuta da sojojin.

    Dakarun Isra'ila na kai manyan hare-hare a sansanin ƴan gudun hijira na Jenin da ke kusa da wurin.

    Rundunar sojin ta ce ta kashe mutane 50 zuwa yanzu waɗanda ta bayyana a matsayin 'ƴan ta'adda'.

    Ofishin shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas ya ce hare-haren ''kisan ƙare dangi' ne, kuma ya yi kira ga Amurka da ta shiga tsakani.

  15. An kashe wani mutum a Ghana saboda gardama kan ƙwallo

    Wani mai goyon bayan ƙungiyar kwallon kafa ta Asante Kotoko, ɗaya daga cikin manyan ƙungiyoyin ƙwallon kafa a Ghana, ya mutu bayan daɓa masa wuƙa da aka yi a wani wasa da ƙungiyarsa ta buga da ƙungiyar Nsoatreman.

    An kashe Francis Yaw Frimpong, wanda aka fi sani da Pooley, ne bayan wata zazzafar gardama ta kaure tsakanin shi da wani mutum da ba a san ko wane ne ba a lokacin da ake buga ƙwallon, a cewar sanarwar da Nsoatreman ta fitar.

    ''Asarar rai ba gaira ba dalili abu ne maras daɗi,'' in ji ƙungiyarsa ta Asante Kotoko.

    Rikice-rikice a filayen ƙwallon ƙafa batu ne da ke cigaba da zama matsala a Ghana inda a 2001, wata tarzoma da aka samu a Accra, babban birnin ƙasar ta yi sanadiyyar kashe mutane aƙalla 120.

    A wasan ranar Lahadi a birnin Nsoatre ma an samu rikicin magoya baya inda mutane ke ta jefa abubuwa cikin filin.

    Lamarin ya tsananta a lokacin da ƴan kallo suka kutsa cikin filin suka kai hari kan ƴan wasa da jam'ai.

    Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Asante Kotoko ta ce mai tsaron gidanta, Mohammed Camara ya fuskanci cin zarafi daga mutanen da suka kutsa cikin filin wasan lokacin da ake rikicin.

    An cigaba da wasan bayan zuwa hutun gajeren lokaci inda ƙugiyar Asante Kotoko ta yi rashin nasara a hannun Nsoatreman bayan da aka tashi 1-0.

    Ƙungiyoyin biyu sun yi allawadai da rikicin da aka samu.

  16. Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo ta dakatar da amfani da shafukan X da Tiktok

    Ba tare da sanarwa ba, hukumomi a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo sun dakatar da amfani da kafafen sada zumunta kamar X da TikTok da kuma amfani da VPN tun a ranar 1 ga watan Fabrairu.

    Ana ganin sun ɗauki matakin ne da niyyar daƙile yaɗuwar labaran ƙarya kan yaƙin da ake yi a gabashin ƙasar, sai dai ƙwararru na gargaɗin hakan zai ta'azzara yaɗa labaran ƙaryan maimakon daƙile shi.

    Kafar yaɗa labaran Faransa, RFI ta ruwaito cewa a ranar 4 ga watan Fabrairu, alamu na nuna cewa kafafen sada zumunta kamar su X da TikTok sun daina aiki a wasu birane a ƙasar tun ranar 1 ga watan Fabarairu.

    Hukumomi a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo sun sanya takunkuman sadarwa tun lokacin da ƴan tawayen M23 suka karɓe iko da birnin Goma a ranar 27 ga watan Janairu.

    Kafar yaɗa labarai ta RFI ta ce ta tattauna da mutane a Goma da Lubumbashi da Kalemie da Bukavu da kuma Kinshasa, inda duk suka ce ba sa iya shiga kafafen X da Tiktok a kan wayoyinsu.

  17. Yadda cutar kansa ta sanya aka rufe min dubura

    Albarkacin ranar yaƙi da cutar, mun tattauna da Maimurna Yampa Barau, wadda ta yi bayani kan yadda ta warke daga cutar daji ta hanji duk da irin illolilin da cutar ta yi mata, ciki har da sauya mata hanyar yin bayan-gida.

  18. An yanke wa mutum biyar hukuncin kisa a Kano bayan kashe tsohuwa bisa zargin maita

    Wata babbar kotu da ke Kano a Najeriya ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan kama su da laifin kisan wata tsohuwa bisa zargin maita.

    Kotun ta ce ta samu mutanen da laifin yin silar mutuwar tsohuwar mai shekara 67 a duniya a ranar 15 ga watan Nuwamban 2023, ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba.

    A lokacin yanke hukuncin, mai shari'a Usman Na'abba ya bayyana cewa kotun ta samu hujjoji ƙarara da suka tabbatar da laifin waɗanda ake tuhuma.

    Lamarin dai ya faru ne a ƙauyen Daɗin Kowa da ke ƙaramar hukumar Wudil ta jihar Kano.

    Maita da tsafi abubuwa ne da ke yawan janyo cece-ku-ce a ƙasashen Afirka, inda iyalai kan ɗauki mataki kan mutanen da suke zargi da kashe musamman yara ta hanyar maita.

  19. Majalisar Dokokin Najeriya za ta koma zama a yau

    A yau Talata ne ake sa ran majalisar wakilan Najeriya za ta koma zama a zauren majalisar, bayan hutun da da ta tafi a watan da ya gabata.

    Bayan zaman ta na farko na shekarar 2025 a ranar 14 ga watan Janairu, majalisar ta ɗage zama zuwa 28 ga watan domin bai wa kwamitoci damar kammala ayyukansu kan dokar kasafin kuɗi da shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya gabatar a gaban Majalisar.

    Ana sa ran cewa a zaman na yau batun dokar haraji nan mai sarƙaƙiya na daga cikin batutuwan da ƴan majalisar za su mayar da hankali kai.

    Ƙudurin harajin, wanda shugaba Tinubu ya gabatar wa Majalisar a shekarar da ta gabata ya janyo zazzafar muhawar a faɗin ƙasar.

    Lamarin da ya sanya aka jingine yanke hukunci a kansa.

    Daga baya gwamnonin jihohin ƙasar sun yi wa ƙudurin gyaran fuska, kuma da alama shugaban ƙasar ya yi maraba da hakan, inda ya yaba wa gwamnonin sannan ya buƙaci majalisar dokokin ta hanzarta amincewa da dokar.

  20. Kasuwannin hannayen jari na Asiya sun sake farfaɗowa

    Kasuwannin hannayen jari na Asiya sun sake farfaɗowa sakamakon matakin da Amurka ta ɗauka na ɗage harajin da ta shirya laftawa kan Canada da Mexico.

    A Japan, kasuwar hannun jarin Nikkei ta haura fiye da kashi ɗaya da rabi cikin ɗari.

    Yayin da bankin Hang Seng na China ya tashi da kusan kashi uku cikin ɗari.

    Sai dai har yanzu ana sa ran sanya ƙarin haraji kan kayayyakin da China ke fitarwa zuwa Amurka, amma Donald Trump ya ce yana sa ran nan ba da jimawa ba zai tattauna da shugaba Xi Jinping.