Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na yau Talata 4 ga watan Fabrairun 2025

Taƙaitattu

  • Najeriya ta ware fiye da naira biliyan 4 don yaƙi da HIV
  • Mutum huɗu sun mutu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Neja
  • An kashe sojojin Isra'ila biyu a Gaɓar Yamma
  • Majalisar Dokokin Najeriya za ta koma zama a yau
  • An yanke wa mutum biyar hukuncin kisa a Kano bayan kashe tsohuwa bisa zargin maita
  • Kasuwannin hannayen jari na Asiya sun sake farfaɗowa
  • Ƴantawayen M23 sun tsagaita wuta a Congo

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi, Aisha Aliyu Ja'afar, Umaymah Abdulmumin da Ahmad Bawage

  1. Ƴantawayen M23 sun tsagaita wuta a Congo

    Ƴan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda da suka ƙwace iko da birnin Goma na Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo sun sanar da tsagaita wuta daga yau Talata.

    Ƴan tawayen sun ce za su tsagaita buɗe wutar ne saboda dalilai na jin ƙai.

    Sun kuma bayyana cewa ba su da shirin ƙwace wani yanki nan gaba a Congo.

    Majalisar ɗinkin duniya ta ce gawarwaki 900 aka tattaro a kan tituna Goma a makon da ya gabata.

    Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun dade suna kira ga Rwanda da ta janye goyon bayan da take bai wa ƴantawayen, suna masu cewa dubun dubatar mutane ne suka rasa muhallansu.

  2. Buɗewa

    Masu bibiyar mu a wannan shafin da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, muna muku maraba a wannan safiya ta Talata 4 ga watan Fabarairun 2025.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu da sada zumunta: facebook, X, Instagram, WhatsApp da YouTube domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa da kallon hotuna da bidiyo.