Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 10/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 10 ga watan Maris 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

  1. Iran na ci gaba da luguden wuta kan Isra'ila da sansanonin Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran na ci gaba da yin luguden wuta kan Isra'ila da sansanonin Amurka da kuma wasu ƙasashen gabas ta tsakiya, a wani martani ga hare-haren da Amurka da Isra'ila ke kai mata.

    A Bahrain, mahukunta sun ce wuta na ci gaba da ci a babbar matatar man ƙasar, lamarin da ya sa kamfanin man ƙasar ya ayyana wata doka ta yarjejeniyar ƙin daukar asara tsakaninsa da abokan hulda, a yayin da aka shiga wani yanayi na bala'i.

    A Isra'ila, an tabbatar da mutuwar mutum guda, da jikkatar wasu da dama sakamakon makamai masu linzamin da Iran din ke ci gaba da harbawa.

    Shugaban darikar katolika na duniya Paparoma Leo ya roki a kai zuciya nesa, yana cewa galibi tasirin yakin na karewa ne a kan 'yan ba ruwana.

  2. Iran ta yi watsi da ƙudirin Trump na kawo ƙarshen yaƙin ƙasar

    ....

    Asalin hoton, Tasnim News Agency

    Rundunar juyin juya halin Iran ta yi watsi da kalaman Shugaba Trump na cewa yakin da Amurka da Isra'ilar suka kaddamar kan Iran din ya kusa zuwa karshe.

    Kalaman na zuwa ne a yayin da shugaba Trump ya shaidawa mahalarta wani taro a Florida cewa Amurka ta samu gagarumar nasara a yaƙin, don haka akwai yiwuwar kawo karshensa nan kusa.

    Da yake jaddada dalilin kai harin, shugaban na Amurka ya ce Iran tana shirin kai hari kan Amurka, ba tare da ya bayar da wata kwakkwarar shaida ba.

    Ya ƙara da cewa Iran ɗin ta yi ta ƙoƙarin sake farfado da shirinta na Nukuliya.

    Da yake amsa tambaya a kan ko Amurka za ta kai hari kan sabon jagoran adddinin kasar Ayatollah Mojtaba Khamenei, Trump ya ce ba abu ne da ya kamata ya furta ba, ko da yake ya bayyana rashin jin dadinda kan zabin na sa.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Talata.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.