Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/08/2025.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Ahmad Bawage da Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Ƙungiyar NATO ta jinjinawa ƴan Ukraine bisa jajircewarsu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar tsaro ta NATO ta jinjina wa abin da ta kira ƙarfin halin ƴan Ukraine wajen kare ƙasarsu, bayan wata tattaunawa ta intanet da gamayyar hafsoshin sojojin ƙasashen ƙungiyar suka yi.

    Shugaban kwamitin hafsoshin sojojin NATO, ya ce sun yi tattaunawa mai muhimmanci kuma sun nuna haɗin kai a ƙoƙarin su na samar da zaman lafiya mai ɗorewa kuma bisa adalci.

    Wakilin BBC ya ce har yanzu Rasha na bayyana cewa ba za ta amince da aika dakaru daga ƙasashen NATO zuwa Ukraine ta kowace fuska ba.

    Rashan ta kuma bayyana duk wata tattaunawa da ba a sanya ta ciki ba a matsayin 'taron shan shayi'

  2. Dakarun RSF sun zargi sojoji da kashe fararen hula a Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun RSF na Sudan sun zargi sojojin ƙasar da kashe fararen hula da kuma lalata motocin da ke ɗauke da kayan agaji a yankin Darfur.RSF ɗin sun ce sojojin sun kai wa wani jerin gwanon motocin shirin samar da abinci na Majalisar ɗinkin duniya guda 16 hari a birnin Malit, inda harin ya kashe mutane da dama wasu kuma suka jikkata.Zuwa yanzu sojojin ba su ce komai ba kan wannan zargi ba.

    Ƙasashe da dama ciki har da Amurka da haɗɗaɗiyar daular larabawa sun fitar da wata sanarwa da ke buƙatar ɓangarorin biyu su dakata da yaƙin domin a samu shigar da kayan agaji.

  3. Amurka ta ƙaƙabawa jami'ian kotun ICC takunkumai

    ICC

    Asalin hoton, Getty Images

    Amurka ta ƙaƙaba takunkumai kan ƙarin jami'an kotun hukunta manyan laifuka ta duniya (ICC) guda 4, kan abin da ta kira barazanar da su ke yi wa Amurka da Isra'ila.

    Jami'an kotun da lamarin ya shafa sun haɗa da mai shari'a Kimberly Prost ƴar Canada, wadda ta bayar da umarnin yin bincike kan wasu ma'aikatan Amurka a Afghanistan, da mai shari'a Nicolas Yann Guillou, da ya bada sammacin kama firaminista Benyamin Netanyahu da tsohon ministan tsaron ƙasar, kan abin da ake zarginsu da aikatawa a Gaza.

    Kotun ta bayyana takunkuman a matsayin wani abu da ke ƙoƙarin yi wa ƴancinta karan-tsaye.

    Wakilin BBC ya rawaito cewa Amurka da Isra'ila ba su amince kotun hukunta manyan laifukan na da hurumi a kansu ba.

    An kuma ƙaƙabawa mataimakan masu shigar da ƙara biyu (Nazhat Shameem Khan da Mame Mandiaye Nian) takunkumai saboda goyon bayan matakin kotun ta ICC kan Isra'ila.

  4. Shugaba Tinubu ya cire harajin kashi biyar kan ɓangaren sadarwa - NCC

    ...

    Asalin hoton, TINUBU/TWITTER

    Shugaba Bola Tinubu ya soke harajin kaso 5 cikin ɗari na harajin da ake ta cece-kuce a kai kan ayyukan sadarwa, matakin da ke da nufin rage matsin tattalin arziki da masu amfani da kafafen sadarwa a ƙasar ke fuskanta.

    Mataimakin shugaban hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC), Aminu Maida ne ya sanar da hakan yayin wani taron manema labarai a Abuja.

    Maida ya tabbatar da cewa harajin wanda da farko aka dakatar da shi a shekarar 2023—a yanzu an cire shi baki ɗaya a hukumance ƙarƙashin dokokin haraji na kasa da aka yi wa kwaskwarima.

    Harajin, wanda ya shafi ayyukan sadarwa na wayar hannu, ya fuskanci suka daga masu ruwa da tsaki, waɗanda suka yi iƙirarin hakan zai ƙara tsadar yin amfani da wayar hannu da duka abubuwan da suka shafi ɓangaren sadarwa a ƙasar.

    Shugaba Tinubu ya fara dakatar da harajin ne a watan Yulin 2023 a matsayin wani ɓangare na sake fasalin tsarin kasafin kuɗi da nufin rage tasirin haraji da yawa kan ƴan kasuwa da ɗaukacin ƴan Najeriya.

    Amma batun ya sake kunno kai a watan Oktoban 2024, lokacin da Majalisar Dokoki ta ƙasa ta ba da shawarar maido da haraji a matsayin wani ɓangare na manyan matakan samar da kuɗaden shiga, wanda ya haɗa da haraji kan wasanni da ayyukan caca.

  5. Gomman ƴan Afghanistan da aka kora daga Iran sun mutu a hatsarin mota

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani hatsarin mota da aka yi a yammacin Afganistan ya yi sanadiyar mutuwar mutane 79 ciki har da ƙananan yara 17, waɗanda akasarinsu suna cikin motar safa ne da ke ɗauke da bakin haure ƴan ƙasar Afghanistan da aka kora daga Iran.

    Kakakin ma'aikatar harkokin cikin gidan Taliban ya tabbatar wa BBC cewa motar bas ɗin da ke kan hanyar zuwa birnin Kabul ta kama da wuta a daren Talata bayan ta yi karo da wata babbar mota da babur a lardin Herat.

    A cewar Ahmadullah Mottaqi, daraktan yaɗa labarai da al'adu na ƙungiyar Taliban a Herat, duka mutanenn da kle cikin bas ɗin sun mutu, da kuma mutane biyu da ke cikin sauran motocin.

    A cikin ƴan watannin nan Iran ta ƙara ƙaimi wajen korar ƴan gudun hijirar Afganistan da ba su da izinin zama a ƙasar, waɗanda suka tsere daga rikici a ƙasarsu.

    Hatsarin mota ya zama ruwan dare a ƙasar Afganistan, inda tituna suka lalace sakamakon rikice-rikicen da aka shafe shekaru da dama ana yi, kuma ba a tsanantawa wurin tabbatar da bin dokokin tuƙi.

    Tun cikin shekarun 1970, miliyoyin ƴan Afghanistan suka yi gudun hijira zuwa Iran da Pakistan, a lokacin mamayar da Tarayyar Soviet ta yi wa Afganistan a shekarar 1979 da kuma bayan komawar Taliban kan karagar mulki a shekarar 2021.

  6. An kashe jagoran ƙungiyar IS a Siriya - Rahotanni

    Rahotanni daga Syria na bayyana cewa an kashe jagoran ƙungiyar IS a Syria, a wani hari da aka kai cikin dare a lardin Idlib da ke ƙasar.

    Wata majiyar tsaro ta faɗa wa gidan talabijin na ƙasar cewa Amurka tare da masu yaƙi da ƙungiyoyin jihadi ne suka far wa gidan jagoran na IS ɗan asalin Iraqi, Salah Numan wanda aka fi sani da Ali - wanda ake zarginsa da hannu a haɗa kan ƴan IS a gidajen yarin Syria.

    Majaiyar tsaron ta ce an harbi Ali har lahira lokacin da ya yi ƙoƙarin tserewa daga gidansa.

    Shaidu sun faɗa wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa sun jiyo ƙarar jirgin sama da kuma harbe-harbe.

    Ƙungiyar IS dai ta ƙwace ikon yanki mai girma a Syria da Iraqi a 2014 lokacin yaƙin basasar Syria, kafin a ci galabarta daga baya.

  7. Fadar Kremlin ta ja-baya daga batun tattaunawa da Zelensky

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar Kremlin ta yayyafa ruwan sanyi kan batun yiwuwar tattaunawar da ake shirin yi tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin da na Ukraine Volodymyr Zelensky, yayin da Donald Trump ya sake sabunta kiran da ya yi na shugabannin biyu su gana domin tattauna kawo ƙarshen yaƙin da ake gwabzawa tsakanin ƙasashensu.

    Yunƙurin tabbatar da ganawar shugabannin biyu ya zo ne bayan da shugaban Amurka ya gana da Putin a Alaska a makon da ya gabata, kuma ya karɓi baƙuncin shugabannin Turai bakwai da Zelensky a fadar White House ranar Litinin.

    Trump ya yarda cewa rikicin "mai sarƙaƙiya" ne kuma ya amince da yiwuwar shugaban na Rasha ba ya da sha'awar kawo ƙarshen tashin hankalin.

    Duk da cewa da farko ya matsa ƙaimi kan taro na ɓangarori uku, amma yanzu Trump yana ba da shawarar cewa zai fi kyau idan shugabannin biyu su ka haɗu ba tare da shi ba.

    Ya ƙara da cewa zai halarci taro da su "idan ya cancanta", amma yana son ya ga "abin da zai faru" tukunna.

  8. Isra'ila ta ce mayaƙan Hamas sun jikkata sojojinta uku

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce mayaƙan ƙungiyar Hamas sun kai hari wani yanki a kudancin Gaza a safiyar yau Laraba, a wani hari da ba a saba ganin irinsa ba.

    Ta ce mayaƙan da suka kai harin sun kai 18, inda suka jikkata sojojin ƙasar uku, ɗaya ya samu munanan raunuka.

    Sai dai sojojin Isra'ilar sun ruwaito kashe yawancin mayaƙan.

    Hamas ta ce dakarunta sun kai hari ne kan wani sabon yanki da Isra'ila ta kafa a Khan Younis, inda suka ruwan bama-bamai da kuma alburusai.

  9. Ƴan Najeriya miliyan 31 na fuskantar matsalar ƙarancin abinci - MDD

    Matsalar ƙarancin abinci

    Asalin hoton, Getty Images

    Ofishin hukumar kula da jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta nuna damuwa kan ƙaruwar yunwa da talauci da kuma rashin tsaro a Najeriya, inda ta yi kiyasin cewa ƴan ƙasar miliyan 31 na fama da matsalar ƙarancin abinci.

    Hukumar ta ce akwai sama da yara miliyan goma ƴan ƙasa da shekara biyar da ke fama da rashin abinci mai gina jiki.

    Bayanin haka ya fito ne a taron da gwamnatin tarayya da hukumar suka gudanar yayin bikin ranar Jin-Ƙai ta Duniya na 2025, wanda aka gudanar ranar Talata a Abuja, mai taken "ƙarfafa haɗin gwiwa a duniya da kuma tallafawa al'ummomi".

    Hukumar ta ce ya kamata a ɗauki matakai cikin gaggawa domin rage barazanar ƙaruwar matsalar.

    Jami'in hukumar ta jin-ƙai a Najeriya, Mohamed Fall, ya bayyana cewa bikin ranar ta bana ya zo ne a daidai lokacin da ake samun raguwar bayar da taimakon jin-ƙai ga mabuƙata a duniya.

    "Buƙatar jin-ƙai na ƙaruwa a Najeriya, sakamakon matsalar ƙarancin abinci da rashin abinci mai gina jiki. Yanzu akwai ƴan Najeriya miliyan 31 da ke fama da matsalar ta ƙarancin abinci," in ji shi.

  10. Isra'ila za ta gina matsugunai 3,500 a Gaɓar Yamma

    Gaɓar Yamma

    Asalin hoton, Reuters

    Isra'ila ta amince da gina wani matsuguni a yankin Gaɓar Yamma da kogin Jordan inda za a gina kusan gidaje 3,500, lamarin da zai raba yankin Falasɗinawa zuwa gida biyu.

    Ministan kuɗi na Isra'ila mai tsattsauran ra'ayi, Bezalel Smotrich ya ce gina unguwar (E1) zai kawar da duk wani shiri na samar da ƙasar Falasɗinawa.

    Matakin na Isra'ila ya sha suka daga ƙasashen duniya, ciki har da ƙawayen Isra'ila da suka bayyana hakan a matsayin tsantsar saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin hakan zai kawo ƙarshen burin kafa ƙasashe biyu.

  11. Dalilin da ya sa kotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele Kyari

    Mele Kyari

    Asalin hoton, Getty Images/EFCC/X

    Wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja babban birnin Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da wasu asusan da ke da alaƙa da tsohon shugaban kamfanin mai na NNPCL Mele Kyari.

    Kotun ta bayar da umarnin dakatar da asusan na bankin Jaiz saboda zargin zamba da kuma halasta kuɗin haram.

    Mai Shari'a Emeka Nwite ne ya bayar da umarni bayan wani lauyan hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci, Ogechi Ujam, ya nemi kotun ta dakatar da amfani da asusan har zuwa lokacin da hukumar za ta kammala bincike a kansu.

    Latsa nan don sanin dalilan...

  12. 'Ba mu cire arewa maso yamma cikin waɗanda za su ci gajiyar wankin ƙoda ba'

    Likitoci

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar lafiya ta tarayya ta musanta rahotanni da ke cewa babu marasa lafiya daga arewa maso yamma cikin waɗanda za su ci gajiyar shirin rage farashin wankin ƙoda da gwamnatin ƙasar ta amince da shi ba.

    Wata sanarwa da ma'aikatar ta wallafa a shafinta na X, ta ce labarin ba shi da kamshin gaskiya.

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ne dai ya amince da rage farashin wankin ƙoda a manyan asibitocin tarayya a faɗin ƙasar.

    Karkashin tsarin, za a rage farashin wankin ƙoda daga naira 50,000 zuwa naira 12,000.

    Shirin wanda aka ɓullo da shi karkashin shirin Renewed Hope na kyautata rayuwar ƴan Najeriya, yana cikin ƙoƙari da gwamnatin tarayya ke yi wajen rage wa masu fama da cutukan da suka jiɓanci ƙoda raɗaɗi.

    An fara shirin ne a manyan asibitocin tarayya guda 11 a faɗin ƙasar.

    Asibitocin sun haɗa da:

    • Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano, a jihar Kano
    • Asibitin koyarwa na jami'ar Maiduguri, a jihar Borno
    • Asibitin koyarwa na jami'ar Abubakar Tafawa Balewa, a jihar Bauchi
    • Asibitin koyarwa na jami'ar Jos, a jihar Filato
    • Babban asibitin ƙasa na Abuja
    • Asibitin gwamnati tarayya a Ebute Metta, jihar Legas
    • Babban asibitin koyarwa a Ibadan, a jihar Oyo
    • Asibitin koyarwa na jami'ar Benin, a jihar Edo
    • Asibitin gwamnatin tarayya a Yenagoa, jihar Bayelsa
    • Asibitin koyarwa a Owerri, jihar Imo
    • Asibitin gwamnatin tarayya a Abakaliki, jihar Ebonyi

    Sanarwar ma'aikatar ta lafiya ta ƙara da cewa za a faɗaɗa shirin domin ya kai ga ƙarin asibitocin gwamnatin tarayya a faɗin ƙasar, inda ta ce babu ɗan Najeriya da za a bari a baya wajen cin wannan gajiya.

    "Gwamnatin tarayya na ci gaba da hobbasa wajen ganin ta rage barazanar kamuwa da cutuka da kuma kare lafiyar duka ƴan Najeriya," in ji ma'aikatar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  13. Sayan kuri'u babbar barazana ce ga dimokraɗiyyar Najeriya - Obi

    Peter Obi

    Asalin hoton, Peter Obi

    Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi ya yi gargaɗi kan masu sayan kuri'u, inda ya kwatanta hakan da cewa barazana ce ga dimokraɗiyyar Najeriya.

    A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce waɗanda ke sayan kuri'u suna so ne kawai su kai ga duƙiyar al'umma domin yin almundahana.

    A cewarsa, kuɗaɗen da aka ware don gina makarantu da asibitoci da kuma hanyoyi na karewa da shiga aljihun ƴan siyasa masu sayan kuri'u da zarar sun shiga ofis.

    "Waɗannan mutane ba shugabanni bane, masu satar duƙiyar ƙasa ne. Ɗabi'unsu na yi wa al'umma lahani da kawo cikas wajen samar da cigaba," kamar yadda Obi ya rubuta.

    Tsohon gwamnan jihar Anamba ya kuma soki masu kaɗa kuri'u waɗanda ke sayar da kuri'unsu don kuɗi, inda ya ce suna sayar da makomarsu ce.

    "Idan ka sayar da kuri'arka, tamkar kana sayar da makarantun da ya kamata ƴaƴanka su je ne da asibitoci da ya kamata su ceci rayuka da kuma ayyuka da za su inganta iyalai da fitar da su daga kangin talauci," a cewar Obi.

    Ya buƙaci ƴan Najeriya su daina sayar da kuri'unsu don zaɓar ƴan siyasar da za su kawo cigaba a ƙasar.

  14. Ba za mu yanke hulɗa baki-ɗaya da hukumar IAEA ba - Tehran

    Iran

    Asalin hoton, EPA

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya ce Tehran ba za ta yanke hulɗa baki-ɗaya da hukumar sa ido kan nukiliya ta duniya ba, don haka za a bar masu sa ido na hukumar su shiga tashoshin nukiliyar ƙasar.

    A watan da ya gabata, majalisar dokoki ta Iran ta amince da wani ƙudiri na yanke hulɗa da hukumar ta IAEA da kuma cewa sai ta samu izini daga majalisar koli ta tsaron ƙasar kafin sa ido kan shirin nukiliyarta ko da nan gaba.

    Masu bincike daga ƙasashen duniya sun kasa samun damar shiga ƙasar don duba na'urorin nukiliyar Iran tun bayan da Isra'ila da Amurka suka far musu, a wani yaƙi na tsawon kwanaki 12 a watan Yuni.

    Iran na da yaƙinin cewa rahoton IAEA a watan Mayu da ya nuna cewa Iran ta saɓa wa batun mallakar makaman nukiliya, shi ya buɗe hanyar kai hare-haren.

  15. Mutanen da suka mutu a hari kan masallaci a Katsina sun kai 30

    Ƴanbindiga

    Asalin hoton, AFP

    Hukumomi a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya, sun ce mutanen da suka mutu a hari da ƴanbindiga suka kai wani masallaci sun kai 30.

    Tun da farko, rahotanni sun bayyana cewa mutum 13 ne aka kashe.

    Ƴanbindigar sun afka wa masallacin ne lokacin da mutane ke sallar asubah.

    Shaidu sun ce ƴanfashin dajin sun kuma far wa wasu garuruwa tare da yin garkuwa da mutane da dama.

    Ana kyautata zaton cewa hari ne na ramuwa bayan ƙwantan ɓauna da ƙauyawa suka yi wa maharan, inda aka kashe da dama daga cikinsu sannan aka saki waɗanda ake garkuwa da su tare da ƙwato makamai.

  16. Lokaci ya ƙure wa Amaechi kan neman takarar shugaban ƙasa - Wike

    Wike

    Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya ce lokaci ya ƙure wa tsohon ministan sufuri Rotimi Amaechi kan yunkurinsa na neman takarar shugabancin Najeriya.

    Wike wanda ya bayyana haka a cikin shirin siyasa na gidan talabijin na Channels Politics Today, ya ce ƴan Najeriya ba za su zaɓi Amaechi a zaɓen 2027 ba.

    Amaechi wanda yake cikin haɗakar jam'iyyar ADC waɗanda ke yunkurin kalubalantar shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027, ya zo na biyu a zaɓen fidda gwani na kujerar shugaban ƙasa na jam'iyyar APC a 2022.

    Amaechi dai ya fice daga jam'iyyar APC zuwa ADC a fafutukar da yake yi na neman kujerar shugaban ƙasa.

    Sai dai, Wike ya ce Amaechi ba zai samu tikiti a jam'iyyar ADC ba don shiga takara a 2027.

    "Amaechi da kansa ya sani cewa ba zai samu tikiti ba. Na ji yana cewa ya san lagon shugaban ƙasa, don haka ya san ta yanda zai kayar da shi. Amma me ya sa ya faɗi a zaɓen fidda gwani a 2022 tun da ya san lagon shugaban ƙasa?", in ji Wike.

    Wike ya soki Amaechi kan kasa yaƙi da cin hanci da kuma rashin shugabanci nagari, inda ya ce bai mutunta ɓangaren shari'a da kuma doka ba lokacin da yake gwamnan jihar Ribas.

  17. Pakistan ta ayyana dokar ta-ɓaci kan ambaliya

    Ambaliya

    Asalin hoton, EPA

    Hukumomi a birnin Karachi na ƙasar Pakistan sun ayyana dokar ta-ɓaci da kuma bai wa ɗalibai hutu sakamakon mamakon ruwan sama da ya ɗaiɗaita birnin.

    Aƙalla mutum takwas ne suka mutu sakamakon ambaliya da aka samu, wadda ta kuma janyo rushewar gidaje da katse layukan bayar da lantarki.

    Ɗaukacin hanyoyin birnin sun cushe sakamakon yawan ruwan da ya jawo cinkoso.

    An yi hasashen cewa za a ci gaba da samun ruwan sama a kwanaki masu zuwa, inda jami'ai ke ta ƙoƙarin ganin sun tallafawa mutane.

    Yankunan arewaci da kuma arewa maso yammacin Pakistan sun fuskanci ambaliya da kuma zaizayar ƙasa.

    Kusan mutum 750 ne suka mutu a wannan shekara a daminar bana a ƙasar, wadda ta fara a watan Yuni.

  18. M23 sun kashe aƙalla fararen hula 140 a Kongo - HRW

    Ƴan tawayen M23

    Asalin hoton, AFP

    Ƙungiyar kare hakkin ɗan'adam ta Human Rights Watch ta ce ta kammala tattara shaidu da ke tabbatar da cewa 'yan tawayen M23 na Kongo sun kashe aƙalla fararen hula 140 a watan da ya gabata, galibi 'yan ƙabilar hutu da suka haɗa maza da mata da kuma yara.

    Kazamin kisan da ake zarginsu da aikata wa a Virunga, shi ne mafi muni da 'yan tawayen suka yi a cikin sama da shekara uku, duk da ƙoƙarin da ake yi na ganin an samar da zaman lafiya a rikicin da ake yi da su a gabashin Congo.

    Ƴan tawayen M23 sun musanta wannan rahoto.

    MDD da wasu majiyoyi daga sojojin Rwanda sun tabbatar da cewa akwai hannun Rwanda a aikata kisan.

  19. 'Zuwa yanzu an ceto mutum 26 bayan hatsarin kwale-kwale a Sokoto'

    Hatsarin kwale-kwale

    Asalin hoton, National Emergency Management Agency (NEMA) Nigeria

    An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar Sokoto, a cewar ɗan majalisar wakilai daga mazaɓar Goronyo/Gada na jihar, Bashir Gorau.

    Ya ce ana fargabar akwai mutum 40 da suka ɓace kawo yanzu bayan da kwale-kwalen ɗauke da fasinjoji sama da 50 ya kife ranar Lahadi.

    "Zuwa yanzu muna ci gaba da bibiyar lamarin, sannan akwai mutanen mu da suka iya ruwa da ke ƙoƙari wajen ganin sun cigaba da ceto sauran mutane. Mun ceto mutum 26 kawo yanzu," kamar yadda ɗan majalisar ya shaida wa gidan talabijin na Channels a wata tattauna ranar Talata.

    Ya kuma ce sun buƙaci hukumomin da ke kula da madatsar ruwa ta Goronyo da su rufe ruwan na tsawon kwanaki biyu don ganin ruwan ya ragu, saboda a ci gaba da aikin ceto.

    Alkaluma da hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA ta fitar tun da farko, sun nuna cewa ana fargabar kusan mutum 40 ne suka rasu a hatsarin.

    Sai dai, Gorau ya yi imanin cewa "babu ainihin alkaluman waɗanda suka ɓace" daga wannan mummunan hatsari.

    "Hasashe ne ake yi cewa mutum 40 ko 50 sun ɓace, sai dai babu takamaimen alkaluman mutanen," in ji ɗan majalisar.

    Ya kuma koka kan yadda ake yawan samun hatsarin jiragen ruwa, inda ya ɗora laifin hakan kan rashin bn matakan kariya na shiga ruwa.

  20. Yadda ƴanbindiga suka kashe masallata 28 a jihar Katsina

    Ƴanbindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, A makon da ya gabata ma rahotonni sun ce 'yanbindigar sun sace tsohon kansila a Malumfashi ta jihar Katsina

    Bayanai na ƙara fitowa game da harin 'yanfashin daji da ya kashe kusan mutum 30 a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya yayin da suke tsaka da sallah a wani masallaci.

    Wasu mazauna yankin Gidan Mantau na ƙaramar hukumar Malumfashi sun shaida wa BBC Hausa cewa lamarin ya faru ne da asubahin ranar Litinin, inda tuni aka yi jana'izar mutum 28.

    "Muna tsaka da sallah suka buɗe mana wuta, mutum 28 muka yi wa jana'iza ciki har da mahaifina," in ji wani mutum da muka ɓoye sunansa cikin kuka da share hawaye.

    Latsa nan don karanta cikakken labarin...