Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/12/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/12/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Harin bam a mota ya kashe wani janar ɗan Rasha

    ...

    Asalin hoton, Russia's Investigative Committee

    Jami'ai a Rasha sun ruwaito cewa wani janar ɗan Rasha ya mutu sakamakon fashewar bam da aka dasa a ƙarƙashin motarsa a birnin Moscow, a cewar jami’ai.

    Kwamitin bincike na Rasha ya ce Laftanar Janar Fanil Sarvarov, mai shekaru 56, ya rasu da safiyar Litinin bayan da aka dasa masa bam ƙarƙashin motarsa.

    Sarvarov shi ne shugaban sashen horas da aikin soja na rundunar sojin Rasha, in ji kwamitin.

    Hukumomin sun ce ɗaya daga cikin ra’ayoyin da ake bincike a kai shi ne yiwuwar dasa bam ɗin da hannu ko taimakon jami’an leƙen asirin Ukraine.

    Ukraine ba ta yi wata magana ba game da lamarin.

  2. Najeriya ta yi asarar kusan naira tiriliyan ɗaya sakamakon harajin Trump - NBS

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/X

    Najeriya ta yi asarar kusan naira biliyan 940.98 a fitar da kayayyaki zuwa Amurka a cikin watanni tara na farkon shekarar 2025 bayan ƙarin harajin shugaban Amurka, Donald Trump, kamar yadda bayanan Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) suka nuna.

    Bayanan NBS sun bayyana cewa "Daga watan Janairu zuwa Satumba na 2025, Najeriya ta fitar da kayayyaki na kimar naira tiriliyan 3.65 zuwa Amurka, ƙasa da naira tiriliyan 4.59 da aka fitar a daidai wannan lokaci a 2024."

    Wannan na nufin an samu raguwar kashi 20.5 kenan.

    Wannan koma-baya ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin Amurka ta fara aiwatar da sabon tsarin haraji inda shugaban Amurka, Donald Trump, ya ƙara harajin Najeriya daga kashi 14 zuwa kashi 15 cikin ɗari.

    Harajin dai ya fara aiki ne a ranar 7 ga Agustan 2025 wanda ya fi shafar kayayyakin da ba na mai ba da Najeriya ke fitarwa.

    A lokaci guda kuma, "Shigo da kayayyaki daga Amurka zuwa Najeriya ya ƙaru sosai zuwa naira tiriliyan 6.80 daga naira tiriliyan 3.01, ƙarin kashi 125.5 cikin 100 wanda ke nuna cewa Najeriya ta sayi kayayyaki daga Amurka fiye da yadda ta sayar mata a shekarar 2025." NBS ta ƙara da cewa.

  3. Kisan mutum 15 ya janyo neman taƙaita mallakar bindiga a Australia

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokokin jihar New South Wales a Australia na gudanar da mahawara kan sauye-sauyen da ake son ɓullo da su a jihar kan mallakar bindiga, bayan kisan mutane da dama da aka yi a wani wajen bikin addinin Yahudawa a wajen bakin teku na Bondi a makon da ya wuce.

    Harin dai ya kashe kashe mutum 15.

    Ƙudurin wanda ake sa ran ya samu karɓuwa, ya haɗa da taƙaita yawan bindigogin da mutum zai iya mallaka.

    Ƙungiyar masu neman bayar da 'yancin mallakar bindiga ta ce ana gaggawar neman aiwatar da ƙudurin - kuma zai shafi waɗanda masu sanin ya kamata da suka mallaki bindiga.

    A matakin tarayya kuma Firaministan kasar ta Australia Anthony Albanese, ya ce zai nemi ganin an yi sababbin dokoki na yaki da tsattsauran ra'ayi da kalamai na kiyayya.

  4. Yadda aka kubutar da sauran ɗaliban makarantar St. Mary da ke jihar Neja

    ...

    Hukumomi a Najeriya sun ce an sako sauran dalibai 130 da aka yi garkuwa da su a jihar Neja.

    Wasu 'yan bindiga ne suka sace daliban da ma'aikatan makarantar ta Katolika ta Saint Mary a a watan da ya gabata.

    Mai magana da yawun shugaban kasa, Sunday Dare a shafinsa na X ya sanar cewa a: yanzu: 'Ba bu wani dalibi ko ma'aikacin makarantar da aka bari a hannun yan bindga'.

    Mai makarantar kuma shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen jihar Neja, Bishop Bulus DauwaYohanna, ya shaida wa BBC cewa Gwamnan jihar Neja ya tabbatar masa da alamarin:

    "Gwamna ya kira ni yanzu inda ya sanar da ni cewa an sako sauran 'yan makaranta da malamai. Ya ce na zo na karbe su," in ji shi.

  5. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu ci gaba daga inda muka tsaya a jiya na labaran kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a cikin Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.