Majalisa ta gayayci shugaban hukumar Kwastam kan ƙin yi wa wasu ritaya
Kwamitin majalisar wakilan Najeriya, da ke karbar koken al'umma ya gayyaci shugaban hukumar Kwastam na kasa, Adewale Adeniyi a gabanta kafin ranar Talatar mako mai zuwa.
Gidan talabijin ta Channels ya rawaito cewar, Chooks Oko, ya ce tilas ne Adeniyi ya bayyana a gaban kwamitin don ya kare kansa daga wani koke da ake yi akan nasa na gaza yi wa wasu jami'an hukumar ritaya, duk da cewar lokacin barinsu aiki ya cika.
Gidauniyar Obasi-Pherson ce dai ta shigar da koken ta gaban majalisar ta 10, inda suka yi zargin cewar mataimakan kontirola da lokacin ajiye aikinsu ya yi har yanzu sun ki ajiyewa.
A wani ci gaban kuma Sanarwar ta Oko ta kuma ce kwamitin ya yi barazanar bayar da umarnin da aka kama shugaban hukumar katin dan kasa NIMS ida ta gaza bayyana a gabanta don amsa wasu tambayoyi, da suka shafi gaza biyan kudin aikin da wani kamfani mai zaman kansa ya yi.