Hamas za ta saki waɗanda take garkuwa da su idan yanayi ya daidaita - Jami'an ƙungiyar
Hamas ta ce "tana ci gaba da jajircewa kan aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta" amma ta jaddada cewa Isra'ila ce ke da ''alhakin duk wani rikici ko jinkiri da za a samu''.
Wani babban jami'in ƙungiyar, Basem Naim ya shaida wa BBC cewa ƙofar ƙungiyar a buɗe take ga Amurka da Qatar da kuma Masar masu shiga tsakani, da su sanya baki domin komawa aiki da yarjejeniyar.
"Ba ma fatan wannan yarjejeniya ta wargaje," a cewarsa. "Muna yin duk mai yiwuwa don kauce wa duka wani abin da zai kawo tarnaƙi ko barazana ga yarjejeniyar, don haka a shirye muke mu miƙa fursunonin da ke hannunmu a ranar Asabar mai zuwa idan masu shiga tsakanin suka daidaita lamura''.
Haka kuma ƙungiyar ta yi fatali da shirin Donald Trump na ''karɓe ikon'' Gaza, tana mai kiran kalaman shugaban da ''wariyar layunin fata'', sannan ta ce shirin ba zai yi nasara ba.