Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 03/13/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 03/13/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Isiyaku Muhammed da Umar Mikail

  1. Faɗa ya sake ɓarkewa tsakanin sojojin Sudan da RSF a kudancin tsakiyar ƙasar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni na cewa ana ƙazamin fada a yankin kudancin tsakiyar Sudan tsakanin rundunar sojin kasar da kuma kungiyar RSF.

    Sojojin sun ce sun ƙwace garin Mabsouta da ke kudancin Kordofan, amma kuma dakarun rundunar da ke Arewacin Kordofan din na fama da harin jiragen sama marassa matuka.

    Mazauna babban birnin - El-Obeid, sun ce sun ga hayaki na tashi daga wani sansanin soji da ke birnin.

    Duk wani yunƙuri na dakatar da bude wuta ya ce tura inda bangarorin biyu ke kafewa kan wasu sharudda da ba za su yiwu ba.

    Jihohin Kordofan din uku sun kasance fagen-daga a yakin basasar Sudan din na wata talatin , ind a yanzu kungiyar ta RSF ta kame Darfur. do a headline for this

  2. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu ci gaba daga inda muka tsaya a jiya na Talatan kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a cikin Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.