KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 12/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 12 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. NiMet ta yi gargaɗin ambaliya a Sokoto, Kaduna, Neja da wasu jihohi 10 a watan Agusta

    .....

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi gargaɗin yiwuwar aukuwar ambaliyar ruwa a jihohi 13 tsakanin ranar 11 da 20 ga watan Agustan 2026.

    Jihohin da ta ce ke fuskantar barazanar sun haɗa da Sokoto, Zamfara, Kebbi, Neja, Kaduna, Nasarawa, Adamawa, Filato, Benue, Kogi, Taraba, Cross River da Akwa Ibom.

    Hukumar ta ce hasashen ya samo asali ne daga nazarin yawan ruwan sama da ake sa ran samu, yanayin danshin ƙasa, ƙarfin magudanan ruwa, yanayin ƙasa da kuma yanayin madatsun ruwa.

    Ta yi gargaɗin cewa ambaliyar ka iya shafar yankunan da ke fama da ambaliya, ƙananan wurare, birane da kuma al'ummomin da ke kusa da koguna, lamarin da zai iya haddasa rufe hanyoyi da tsaikon sufuri.

    NiMet ta kuma ce ambaliyar na iya lalata gonaki, amfanin gona da dabbobi tare da shafar wutar lantarki da hanyoyin sadarwa.

    Hukumar ta shawarci jama'a su riƙa bibiyar hasashen yanayi da gargaɗin ambaliya, su guji wucewa ta hanyoyin da ruwa ya mamaye, yayin da ta buƙaci hukumomin agajin gaggawa da manoma su ɗauki matakan kariya domin rage illolin da ka iya tasowa.

  2. 'Yan Pakistan uku sun mutu a harin Houthi kan wani jirgin ruwa

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan Harkokin Wajen Pakistan, Mohammad Ishaq Dar, ya sanar a ranar Laraba cewa 'yan ƙasar Pakistan uku sun mutu sakamakon harin da mayaƙan Houthi suka kai kan wani jirgin ruwa a Tekun Bahar Maliya.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafin X, Ishaq Dar ya ce: "'Yan ƙasar Pakistan uku sun rasa rayukansu, yayin da mutum guda ya jikkata a wannan lamari."

    Kalaman nasa sun zo ne kwana guda bayan hukumomin tsaron gaɓar tekun Yemen suka tabbatar da cewa aƙalla mutum shida ne suka mutu a harin da mayaƙan Houthi suka kai kan wani jirgin ruwa a gaɓar ƙasar.

    Har yanzu ba a bayyana ƙarin cikakkun bayanai kan mutanen da suka mutu ko kuma yanayin jirgin ruwan da harin ya rutsa da shi ba.

  3. Sabon jirgin da aka sauya min ya ma fi haɗarin fuskantar harin Iran - Trump

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce sabon jirgin sojin da aka sauya masa a lokacin da yake komawa Amurka daga Turkiyya ya fi haɗarin fuskantar harin Iran fiye da jirgin shugaban ƙasar Amurka Airforce one da ya bari.

    Da yake magana da manema labarai, Trump ya ce ya bi shawarar hukumomin tsaro inda ya koma Amurka ta wani jirgin daban bayan halartar taron ƙungiyar NATO a Turkiyya kusan wata guda da ya wuce.

    Rahotannin kafofin yaɗa labaran Amurka sun ce jami'an tsaro sun gano wata babbar barazana daga Iran ta yiwuwar harba makami mai linzami kan jirgin Trump lamarin da ya sa ya sauya jirgi a asirce.

    Trump ya kuma yi iƙirarin cewa Amurka ce ke da cikakken iko da Mashigar

  4. Za mu farmaki cibiyoyin Amurka da na ƙawayenta idan aka sake kai mana hari - Iran

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Jami'in dakarun juyin juya halin Iran (IRGC), Hossein Mohebi, ya ce Amurka da ƙawayenta za su fuskanci hare-hare kan muhimman cibiyoyinsu idan aka sake kai wa Iran hari.

    Ya yi gargaɗin cewa Iran za ta iya kai farmaki kan tashoshin samar da wutar lantarki, layukan isar da makamashi da sauran muhimman tsare-tsaren Amurka da na ƙawayenta.

    Mohebi ya kuma ce, manyan sassan cibiyoyin sadarwa na duniya da ke da alaƙa da intanet na iya fuskantar barazana idan aka sake kai wa Iran hari.

    Ya ƙara da cewa a halin yanzu babu wani jirgin ruwa na Amurka da ke cikin ruwan Tekun Fasha.

    Kalaman kakakin IRGC na zuwa ne sa'o'i kaɗan bayan shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba yarda da Iran domin, a cewarsa, tana yi masa ƙarya.

    Trump ya kuma jaddada cewa Mashigin Hormuz yana ƙarƙashin ikon Amurka kuma mallakin Amurka ne.

  5. Assalamu alaikum

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye.

    Kamar kullum, yau ma za mu muku labaran abubuwan da ke faruwa game da yaƙin Iran da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a wannan rana ta Laraba.

    Aisha Babangida ce za ta saka kasancewa da ku daga yanzu zuwa ƙarfe 4 na yamma.

    Za ku iya yin tsokaci a shafukanmu na sada zumunta: Facebook, X, instagram, YouTube da kuma zaurenmu na WhatssApp.

    Ku kasance da mu.