Osimhen, Zaidu da sauran ƴan wasan da za su wakilci Najeriya a Afcon 2025
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya ta fitar da sunayen ƴan wasan Super Eagles da za su wakilci ƙasar a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta Afirka ta 2025 da za ta gudana a Moroco.
Hukumar ta fitar da sunayen ne bayan rairaye su daga cikin ƴan wasa 50 da ta fitar tun farko.
Ƴanwasan Super Eagles ɗin da aka sanar a ranar Laraba su ne:
Masu tsaron raga:
- Stanley Nwabali
- Francis Uzoho
- Amas Obasogie
Masu tsaron baya:
- Calvin Bassey
- Zaidu Sanusi
- Semi Ajayi
- Bruno Onyemaechi
- Igoh Ogbu
- Chidozie Awaziem
- Bright Osayi-Samuel
- Ryan Alebiosu
Ƴan wasan tsakiya:
- Wilfred Ndidi
- Frank Onyeka
- Fisayo Dele Bashiru
- Muhammed Usman
- Alex Iwobi
- Ebenezer Akinsanmiro
- Raphael Anyedika
- Tochukwu Nnadi
Ƴan wasan gaba:
- Ademola Lookman
- Victor Osimhen
- Akor Adams
- Samuel Chukwueze
- Cyriel Dessers
- Salim Fago
- Moses Simon
- Chidera Ejuke
- Paul Onuachu
A ranar 21 ga watan Disamban 2025 ne za a take wasan farko na gasar tsakanin Moroko da Comoros a birnin Rabat.
Najeriya za ta buga wasanta na farko ne ranar Talata 23 ga watan Disamba a birnin Fes, inda za ta kara da ƙasar Tanzaniya.