Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 11/04/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 11/04/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Isiyaku Muhammed da kuma Aisha Bappa

  1. Taliban ta zartar da hukuncin kisa kan wasu mutum uku

    Taliban

    Asalin hoton, Reuters

    Hukummin Taliban a Afghanistan sun zartar da hukuncin kisa a bainar jama'a kan wasu mutum uku a sassan ƙasar.

    An harbe wasu maza biyu a lardin Badghis, yayin da aka kashe na ukun a garin zaranj na lardin Nimroz.

    Cikin wata sanarwa da Taliban ɗin ta fitar ta ce an samu duka mutanen uku da laifin kisan kai sannan aka yanke musu hukuncin kisa.

    Shaidu sun ce rahotonni sun tabbatar da cewa mutanen da aka kashe a Badghis an kashe su ne a gaban dandazon jama'a.

    A watan Nuwamban da ya gabata ne aka aiwatar da hukuncin kisa na ƙarshe da aka aiwatar a Afghanistan.

  2. Kwamitin yaƙi da dabanci a Kano ya ce ya samu nasarar kama ɓatagari sama da 400

    Ƴansanda

    Asalin hoton, Getty Images

    A jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, kwamitin kar-ta-kwana kan yaƙi da ayyukan daba da dawo da zaman lafiya da gyaran halin matasa, ya sanar da kama ɓata-gari fiye da 400.

    Kwamitin ya ce daga cikin waɗanda aka kama ɗin, an yankewa kashi 70 cikin 100 a cikinsu hukunci.

    Matsalar daba da ƙwacen waya dai, sun sa jama'a a Kano na rayuwa cikin firgici tare da ƙauracewa fitar dare da kuma yin taka tsan-tsan da rana kasancewar harin daba na iya rutsawa da mutum a kowane lokaci.

    Dr Yusuf Ibrahim Kofarmata shi ne shugaban kwamitin kuma ya yi wa BBC ƙarin bayani, inda ya ce zuwa yanzu sun samu nasarorin da aka daɗe ba a samu ba.

    Ya ce, "aiki ne babba, amma suna aiki sosai domin shiga lungu da saƙo tare da taimakon jami'an tsaro. Kuma muna da kotun ta fi da gidanka, inda muke yanke hukunci nan take."

  3. Mutum shida sun mutu a hatsarin jirgi mai saukar ungulu a Amurka

    Amurka

    Asalin hoton, Reuters

    Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin - fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.

    Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.

    Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.

    Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.

    Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.

  4. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'atu babbar rana, daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu kawo labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta irin su X da Facebook da Instagram domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo.

    Ku kasance tare da mu.