Wane ne zai gaji jagoran addinin Iran Ayatollah Khamenei?

Asalin hoton, AP
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa Iran na shirin sanar da "sabbin matakai" game da shirinta na nukiliya domin samun damar cimma yarjejeniya da Amurka.
Matakin zai bayar da damar ɗage wa ƙasar takunkumai da kuma amincewa da shirinta na sarrafa makamashin nukiliya ƙarƙashin shirinta na zaman lafiya.
Reuters ya ambato wani babban jami'in gwamnatin Iran na cewa ɓangarorin biyu sun sha bamban a wasu fannoni, ciki har da batun sassauta tsauraran takunkuman Amurka da ke kan ta.
Wannan na zuwa ne yayin da Oman, ƙasar da ke shiga tsakanin ɓangarorin biyu, ta tabbatar cewa za a shiga zagaye na gaba na tattaunawar a birnin Geneva, ranar Alhamis.


