Wane giɓi rasuwar Muhammadu Buhari za ta samar a siyasar Najeriya?

Asalin hoton, Getty Images
Rasuwar tsohon shugaban Najeriya, Muhamamdu Buhari babu shakka ta samar da giɓi a siyasar Najeriya musamman a arewacin ƙasar.
Masu fashin baƙi na ganin rasuwar tsohon shugaban ƙasar ka iya haifar da wani ƙokari daga ƴan siyasar arewacin ƙasar na maye gurbinsa musamman a daidai lokacin da zaɓen shugaban ƙasa na 2027 ke ƙara ƙaratowa.
A yankin arewacin ƙasar an ayi wa Muhammadu Buhari ba kawai a matsayin ɗan siyasa ba har ma da kasancewarsa mahaɗa tsakanin talakawa da masu faɗa a ji.
Mutum ne da yake da mabiya na ga-ni-kashe ni a yankunan karkara da biranen yankin arewacin Najeriya.




