Su wane ne suka lakaɗa wa Danbilki Kwamanda duka a bidiyo?

Asalin hoton, Facebook/Abdulmajid Kwamanda
Wani bidiyon da ya ɓulla a shafukan sada zumunta ya nuna yadda wasu mutane ke dukan ɗan siyasar mai yawan magana a kafofin yaɗa labarai da bulala bayan sun ɗaure hannunsa da ankwa.
An ji mutanen da ba a ganin su a bidiyon na tuhumar sa kan dalilin da ya sa "yake zagin" gwamnan Kaduna Uba Sani, yayin da shi kuma yake musanta zargin.
BBC Hausa ta fahimci cewa lamarin ya faru ne a Abuja ranar Laraba da dare.



